Ruwanda ta sanar da janyewa daga kungiyar CEEAC
Published: 8th, June 2025 GMT
Gwamnatin kasar Ruwanda ta sanar da janyewa daga kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen tsakiyar nahiyar Afirka wato CEEAC, bayan ta zargi jamhuriyyar demokuradiyyar Congo da hada kai da wasu kasashe membobin kungiyar, wajen amfani da kungiyar don neman cimma bukatunsu.
Cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin waje da hadin gwiwar kasa da kasa ta kasar Ruwanda ta fitar, an ce, a gun taron koli na kungiyar ta CEEAC da aka gudanar a birnin Malabo dake kasar Equatorial Guinea, jamhuriyyar demokuradiyyar Congo ta hada kai da sauran kasashe membobin kungiyar, don hana Ruwanda damar karbar ragamar shugabancin kungiyar a wannan karo.
Ma’aikatar ta bayyana cewa an ware Rwanda daga taron koli na 22 na ECCAS da aka gudanar a Kinshasa a shekarar 2023 karkashin jagorancin Kongo, yayin da rikici tsakanin kasashen biyu ke kara tsananta.
Gwamnatin Rwanda ta jaddada cewa wannan yanayin wata sabuwar shaida ce ta “wuce gona da iri” na kungiyar, kuma ba ta wani dalili na ci gaba da kasancewa mamba na wata kungiya da ke aiki ba bisa ka’idoji da amfanin da aka kafa ta ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung
A wannan rana, a gun taron manema labarai da aka gudanar bayan kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar APEC, Lee Jae-myung ya ce hadin gwiwar tattalin arziki tsakanin Sin da Koriya ta Kudu yana da matukar muhimmanci, ya kuma yi imanin cewa birnin Shenzhen na kasar Sin zai karbi bakuncin kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar APEC cikin nasara a shekara mai zuwa.(Safiyah Ma)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA