Ruwanda ta sanar da janyewa daga kungiyar CEEAC
Published: 8th, June 2025 GMT
Gwamnatin kasar Ruwanda ta sanar da janyewa daga kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen tsakiyar nahiyar Afirka wato CEEAC, bayan ta zargi jamhuriyyar demokuradiyyar Congo da hada kai da wasu kasashe membobin kungiyar, wajen amfani da kungiyar don neman cimma bukatunsu.
Cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin waje da hadin gwiwar kasa da kasa ta kasar Ruwanda ta fitar, an ce, a gun taron koli na kungiyar ta CEEAC da aka gudanar a birnin Malabo dake kasar Equatorial Guinea, jamhuriyyar demokuradiyyar Congo ta hada kai da sauran kasashe membobin kungiyar, don hana Ruwanda damar karbar ragamar shugabancin kungiyar a wannan karo.
Ma’aikatar ta bayyana cewa an ware Rwanda daga taron koli na 22 na ECCAS da aka gudanar a Kinshasa a shekarar 2023 karkashin jagorancin Kongo, yayin da rikici tsakanin kasashen biyu ke kara tsananta.
Gwamnatin Rwanda ta jaddada cewa wannan yanayin wata sabuwar shaida ce ta “wuce gona da iri” na kungiyar, kuma ba ta wani dalili na ci gaba da kasancewa mamba na wata kungiya da ke aiki ba bisa ka’idoji da amfanin da aka kafa ta ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Edgar Lungu: Za a yi zaman makokin kwana 7 a Zambiya
Ƙasar Zambiya ta ayyana zaman makoki na kwanaki bakwai don girmama tsohon shugaban ƙasar, Edgar Lungu, wanda ya rasu a ranar Alhamis, 5 ga watan Yuni, 2025, a ƙasar Afirka ta Kudu.
Ya rasu yana da shekaru 68.
Gobara ta tashi a otal ɗin da ke ɗauke da Alhazan Najeriya 480 a Makkah 2027: Makomar Shettima a matsayin abokin takarar Tinubu na janyo cece-kuceLungu ya shugabanci Zambiya daga watan Janairun shekarar 2015 har zuwa watan Agustan 2021, lokacin da ya sha kaye a hannun shugaban ƙasa mai ci yanzu, Hakainde Hichilema.
Gwamnati ta sanar da cewa daga ranar 8 zuwa 14 ga wata Yuni, duk tutocin ƙasar za su kasance a ƙasa, sannan kuma an dakatar da duk wasu tarukan nishaɗi a wannan lokacin domin nuna alhini da mutunta tsohon shugaban.
Sakataren majalisar ministoci, Patrick Kangwa, ya bayyana cewa Shugaba Hichilema ya amince da yi wa Lungu jana’izar ƙasa.
An shirya dawowar gawarsa zuwa Zambiya a ranar Laraba mai zuwa.
Gwamnatin ƙasar ta ce Belvedere Lodge da ke babban birnin Lusaka ita ce cibiyar da aka ware don gudanar da makokin.
Kafin rasuwarsa, Lungu na ƙarƙashin kulawar likita a wani asibiti da ke Pretoria, Afirka ta Kudu.
Jam’iyyarsa ta Patriotic Front (PF) ta ce ya sha fama da wata cuta mai suna “achalasia” wata matsala ce da ke hana abinci wucewa a maƙogwaro yadda ya kamata.