Ruwanda ta sanar da janyewa daga kungiyar CEEAC
Published: 8th, June 2025 GMT
Gwamnatin kasar Ruwanda ta sanar da janyewa daga kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen tsakiyar nahiyar Afirka wato CEEAC, bayan ta zargi jamhuriyyar demokuradiyyar Congo da hada kai da wasu kasashe membobin kungiyar, wajen amfani da kungiyar don neman cimma bukatunsu.
Cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin waje da hadin gwiwar kasa da kasa ta kasar Ruwanda ta fitar, an ce, a gun taron koli na kungiyar ta CEEAC da aka gudanar a birnin Malabo dake kasar Equatorial Guinea, jamhuriyyar demokuradiyyar Congo ta hada kai da sauran kasashe membobin kungiyar, don hana Ruwanda damar karbar ragamar shugabancin kungiyar a wannan karo.
Ma’aikatar ta bayyana cewa an ware Rwanda daga taron koli na 22 na ECCAS da aka gudanar a Kinshasa a shekarar 2023 karkashin jagorancin Kongo, yayin da rikici tsakanin kasashen biyu ke kara tsananta.
Gwamnatin Rwanda ta jaddada cewa wannan yanayin wata sabuwar shaida ce ta “wuce gona da iri” na kungiyar, kuma ba ta wani dalili na ci gaba da kasancewa mamba na wata kungiya da ke aiki ba bisa ka’idoji da amfanin da aka kafa ta ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Yan Majalisar Dokokin Kasashen Iran Da Iraki Sun Amince Da Ra’yin Ficewar Sojojin Amurka Daga Iraki
Yan majalisar dokokin kasar Iran sun bukaci majalisar dokokin kasar Iraki su kori sojojin Amurka daga kasar ta Iraki.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran yana cewa, yan majalisar dokokin kasar Iran sun bayyana haka ne a lokacin ganawasu da wani dan majalisar dokokin kasar Iraki mai wakiltan lardin Karbalar Imam Hussain (a) a majalisar dokokin kasar.
Labarin ya nakalto wakilin lardin Karbala a majalisar dokokin kasar Iraki yana cewa kasashen Iran da Iraki da gwamnatin kasar Iraki sun gamu a wannan ra’ayin kuma nan gaba abinda za’a yi Kenan. Yace dole ne sojojin Amurka su fice daga kasar Iraki, su kuma fice daga dukkan kasasjen larabawa a yankin. Ya ce da haka ne kasashen yankin zasu tabbatar da tsaron yankinsu.
Ebrahim Rezae dan majalisar dokokin kasar Iran ya bayyana cewa, kasar Amurka baa bin Amincewa ne, kuma shirin HKI na fadada mamayar karin yankunan kasashen larabawa na tafiya ne tare da umurnin Amurka kai tsaye.
A ranar 3 ga watan Jenerun Shekara ta 2020 ne shugaban Donal Trump ya bada umurnin kashe babban kwamandan rundunar Qudus ta Iran Janar Shahid Qasim Sulaimani a lokacinda ya shigo kasar Iraki daga Siriya tare da gayyatar gwamnatin kasar ta Iraki.