Sojojin Isra’ila sun kashe mutum 13 a wajen rabon tallafi a Gaza
Published: 7th, June 2025 GMT
Aƙalla Falasɗinawa 13 ne suka rasu a ranar Asabar a Gaza, sakamakon hare-haren da sojojin Isra’ila suka kai.
Mutum shida daga cikinsu sun mutu ne a kusa da cibiyar rabon tallafi a garin Rafah da ke Kudancin Gaza.
2027: Makomar Shettima a matsayin abokin takarar Tinubu na janyo cece-kuce Yadda Sanusi II da Aminu Ado suka yi sallar Idi daban-daban a KanoMai magana da yawun hukumar kashe gobara ta Gaza, Mahmud Bassal, ya ce harin ya faru da misalin ƙarfe 7 na safe, a kusa da gadar Al-Alam.
Mutane sun taru a wajen domin karɓar tallafi daga wata cibiya da Gidauniyar Gaza Humanitarian Foundation (GHF) ke jagoranta, wadda ke samun goyon bayan Amurka, kimanin kilomita ɗaya daga wajen.
Shaidu sun ce, da zarar wasu suka yi ƙoƙarin matsawa kusa da cibiyar agajin, sai sojojin Isra’ila da ke cikin motocin yaƙi su fara harbi a sama, kafin daga baya suka buɗe wa mutane wuta.
Dakarun Isra’ila sun ce suna bincike kan lamarin.
Wannan ba shi ne karon farko da aka kashe mutane a kusa da cibiyar agaji ta Al-Alam ba.
Gidauniyar GHF ta fara rabon tallafin ne tun ƙarshen watan Mayu, bayan Isra’ila ta sassauta wani takunkumi da ta ɗora wa Gaza na sama da watanni biyu.
Majalisar Ɗinkin Duniya dai ta ƙi haɗa kai da GHF saboda rashin tabbas kan adalci, kuma ta yi gargaɗin cewa kusan dukkanin al’ummar Gaza sama da mutum miliyan biyu na fuskantar barazanar yunwa.
A wani ɓangare na Gaza a ranar Asabar, an kuma kashe mutum bakwai sakamakon wani hari da jirgin saman Isra’ila ya kai wani gida kusa da Asibitin Al-Shifa da ke birnin Gaza.
Sojojin Isra’ila sun ce shi ma za su binciki wannan harin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Falasɗinawa Isra ila Rabon Tallafi
এছাড়াও পড়ুন:
Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza
Kasashen duniya na ci gaba da yin tir da sabon farmakin soji da Isra’ila ta kaddamar kan Gaza.
Kasashen Biritaniya, Faransa, Italiya, Masar, Jordan, Qatar, Spain, duk sun yi tir da farmakin kan Gaza suna masu cewa zai kara dagula halin kunci da ake ciki.
Kungiyar tarayyar Turai, ta bakin Jami’ar kula da harkokin wajen ta, Kaja Kalas, ta yi kira da a sanyawa Isra’ila takunkumi domin matsa wa gwamnatin lamba ta kawo karshen hare-haren da take kaiwa Gaza, tana mai gargadin cewa al’amuran jin kai na kara ta’azzara.
“Hare-haren da Isra’ila ta kai a Gaza zasu haifar da mummunan sakamako game da halin da ake ciki da karin hasarar rayuka, da barna & hijira na jama’a,” in ji Kalas a kan X.
A jiya ne Sojojin Isra’ila suka kaddamar da sabon farmakin ta kasa mai manufar mamaye birnin Gaza bayan shafe makwanni ana kai hare-haren bama-bamai ba kakkautawa ba a kan wasu manyan gine-gine domin tilastawa Falasdinawa kauracewa gidajensu.
Farmakin ya zo ne jim kadan bayan da sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya gana da firaminista Benjamin Netanyahu a kusa da masallacin Al Aqsa da ke gabashin birnin Kudus da aka mamaye.
Tun da farko dai, wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya ta musamman kan yankunan Falasdinawa da ke mamaye, Francesca Albanese ta yi Allah wadai da hare-haren da Isra’ila ke kai wa birnin Gaza, tana mai cewa wani bangare ne na shirin Isra’ila na shafe Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran da Saudiyya sun bukaci hadin Musulmi game da halin da ake ci a yankin September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana September 16, 2025 Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi September 16, 2025 Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya September 16, 2025 Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci