Aminiya:
2025-06-07@21:55:47 GMT

Sojojin Isra’ila sun kashe mutum 13 a wajen rabon tallafi a Gaza

Published: 7th, June 2025 GMT

Aƙalla Falasɗinawa 13 ne suka rasu a ranar Asabar a Gaza, sakamakon hare-haren da sojojin Isra’ila suka kai.

Mutum shida daga cikinsu sun mutu ne a kusa da cibiyar rabon tallafi a garin Rafah da ke Kudancin Gaza.

2027: Makomar Shettima a matsayin abokin takarar Tinubu na janyo cece-kuce Yadda Sanusi II da Aminu Ado suka yi sallar Idi daban-daban a Kano

Mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta Gaza, Mahmud Bassal, ya ce harin ya faru da misalin ƙarfe 7 na safe, a kusa da gadar Al-Alam.

Mutane sun taru a wajen domin karɓar tallafi daga wata cibiya da Gidauniyar Gaza Humanitarian Foundation (GHF) ke jagoranta, wadda ke samun goyon bayan Amurka, kimanin kilomita ɗaya daga wajen.

Shaidu sun ce, da zarar wasu suka yi ƙoƙarin matsawa kusa da cibiyar agajin, sai sojojin Isra’ila da ke cikin motocin yaƙi su fara harbi a sama, kafin daga baya suka buɗe wa mutane wuta.

Dakarun Isra’ila sun ce suna bincike kan lamarin.

Wannan ba shi ne karon farko da aka kashe mutane a kusa da cibiyar agaji ta Al-Alam ba.

Gidauniyar GHF ta fara rabon tallafin ne tun ƙarshen watan Mayu, bayan Isra’ila ta sassauta wani takunkumi da ta ɗora wa Gaza na sama da watanni biyu.

Majalisar Ɗinkin Duniya dai ta ƙi haɗa kai da GHF saboda rashin tabbas kan adalci, kuma ta yi gargaɗin cewa kusan dukkanin al’ummar Gaza sama da mutum miliyan biyu na fuskantar barazanar yunwa.

A wani ɓangare na Gaza a ranar Asabar, an kuma kashe mutum bakwai sakamakon wani hari da jirgin saman Isra’ila ya kai wani gida kusa da Asibitin Al-Shifa da ke birnin Gaza.

Sojojin Isra’ila sun ce shi ma za su binciki wannan harin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Falasɗinawa Isra ila Rabon Tallafi

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
  • An Kashe Sojojin HKI Da Dama Sannan Wasu Sun Ji Raune A Garin Khan Yunus A Jiya Jumma
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gargadi Kasashen Turai Kan Fuskantar Martani Daga Kasar Iran
  • Sojoji sun kashe manyan Kwamandojin ISWAP 3 a Borno
  • Mun gurfanar da mutum 29 a kotu kan zargin kashe DPO a Kano – ’Yan sanda
  • Wani mutum ya mutu a cikin rijiya a Kano
  • Shugaban Kasar Rasha Vladimir Putin Zia Kawo Ziyara Tehran Nan Kusa
  • Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ben Gurion Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila