Aminiya:
2025-07-24@04:02:50 GMT

Sojojin Isra’ila sun kashe mutum 13 a wajen rabon tallafi a Gaza

Published: 7th, June 2025 GMT

Aƙalla Falasɗinawa 13 ne suka rasu a ranar Asabar a Gaza, sakamakon hare-haren da sojojin Isra’ila suka kai.

Mutum shida daga cikinsu sun mutu ne a kusa da cibiyar rabon tallafi a garin Rafah da ke Kudancin Gaza.

2027: Makomar Shettima a matsayin abokin takarar Tinubu na janyo cece-kuce Yadda Sanusi II da Aminu Ado suka yi sallar Idi daban-daban a Kano

Mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta Gaza, Mahmud Bassal, ya ce harin ya faru da misalin ƙarfe 7 na safe, a kusa da gadar Al-Alam.

Mutane sun taru a wajen domin karɓar tallafi daga wata cibiya da Gidauniyar Gaza Humanitarian Foundation (GHF) ke jagoranta, wadda ke samun goyon bayan Amurka, kimanin kilomita ɗaya daga wajen.

Shaidu sun ce, da zarar wasu suka yi ƙoƙarin matsawa kusa da cibiyar agajin, sai sojojin Isra’ila da ke cikin motocin yaƙi su fara harbi a sama, kafin daga baya suka buɗe wa mutane wuta.

Dakarun Isra’ila sun ce suna bincike kan lamarin.

Wannan ba shi ne karon farko da aka kashe mutane a kusa da cibiyar agaji ta Al-Alam ba.

Gidauniyar GHF ta fara rabon tallafin ne tun ƙarshen watan Mayu, bayan Isra’ila ta sassauta wani takunkumi da ta ɗora wa Gaza na sama da watanni biyu.

Majalisar Ɗinkin Duniya dai ta ƙi haɗa kai da GHF saboda rashin tabbas kan adalci, kuma ta yi gargaɗin cewa kusan dukkanin al’ummar Gaza sama da mutum miliyan biyu na fuskantar barazanar yunwa.

A wani ɓangare na Gaza a ranar Asabar, an kuma kashe mutum bakwai sakamakon wani hari da jirgin saman Isra’ila ya kai wani gida kusa da Asibitin Al-Shifa da ke birnin Gaza.

Sojojin Isra’ila sun ce shi ma za su binciki wannan harin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Falasɗinawa Isra ila Rabon Tallafi

এছাড়াও পড়ুন:

Yunwa na ƙara tsanani a Arewa maso Gabashin Nijeriya — ICRC

Kungiyar Agaji ta Red Cross (ICRC) ta bayyana cewa yunwa na ƙara tsananta a Arewa maso Gabashin Nijeriya, musamman a jihohin Borno, Adamawa da Yobe.

A cewar rahoton, rikicin da ya dauki shekaru 16 ya durƙusar da kasuwanci da hanyoyin samun aiki, wanda hakan ya tilastawa mutane dogaro da ƙananan gonaki don rayuwa.

Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh Jihohin da za a samu ruwan sama da iska mai ƙarfi a sassan Nijeriya — NiMet

ICRC ta bayyana cewa fiye da mutum miliyan 3.7, wadanda galibi manoma ne na fuskantar barazanar matsanancin rashin abinci a yankin da aka shafe shekaru ana rikici.

Churi Ibrahim, wani tsohon manomi dan shekara 70 da ke ciyar da iyalinsa goma, ya ce farashin abinci ya yi tashin gwauron zabi, kuma kudin ɗinki da yake samu da dare bai isansu.

Modu Umar, wani shugaban al’umma, ya bayyana cewa yunwa tana haddasa cututtuka kamar gudawa a cikin yara da manya saboda rashin abinci da magani.

“Mutane na fita nesa su tara itace domin samun kudin siyan abinci,” in ji shi.

ICRC dai ta ce ta fara wani shiri na taimaka wa noma ta hanyar raba iri da kayan aikin noma ga sama da iyalai 21,000 a bana, domin tallafa musu a lokutan kaka da rani.

“Ana kuma shirin rarraba famfunan ban-ruwa masu aiki da hasken rana domin noman rani,” in ji ƙungiyar ICRC.

Shugabar ofishin ICRC a Maiduguri, Diana Japaridze, ta ce ana fargabar za a fuskanci matsanancin ƙarancin abinci daga Yuli zuwa Satumba, inda mutane ke buƙatar sayen abinci, amma ƙarancin kudi yana hana su cika buƙata.

A cewarta, matsananciyar yunwar na janyo tsamurewar jiki saboda rashin abinci mai gina jiki musamman a tsakanin ƙananan yara ’yan ƙasa da shekaru biyar da kuma mata masu shayarwa.

Ƙungiyar ICRC na aiki a Borno tun 2012 inda take taimaka wa al’ummomin da rikici ya shafa da kuma kare martabar fararen hula bisa dokokin Geneva na 1949.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Sojojin Ruwan Iran Sun Kori Jirigin Yakin Amurka Daga Tekun Oman
  • Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Na Isra’ila Da Makami Mai Linzami Nau’in Flasdinu
  • Sheikh Qasem: Nuna Halin Ko In-Kula Na Duniya Ne Ya Jawo Kisan Kiyashi A Gaza
  • Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa
  • Zazzaɓin Lassa ya kashe mutum 151 a Nijeriya bana — NCDC
  • Yunwa na ƙara tsanani a Arewa maso Gabashin Nijeriya — ICRC
  • Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh
  • WHO Ta Buƙaci Isra’ila Ta Saki Ma’aikacinta Da Aka Kama A Gaza
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kwara Ta Taimaka Wajen Hana Lalacewar Wani Bene A Ilorin