Aminiya:
2025-06-18@02:17:03 GMT

A saurari sauyin da mu yi wa ɓangaren man fetur a Nijeriya — Dangote

Published: 10th, June 2025 GMT

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ya ce nan ba da jimawa ba al’ummar Nijeriya za su ga gagarumin sauyi a ɓangaren man fetur ɗin ƙasar.

Dangote ya bayyana hakan ne yayin ganawa da manema labarai, a lokacin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ziyarci matatar mansa da ke yankin Lekki a Jihar Lagos.

NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Magance Matsalar Kwacen Waya Mijina bai saci kuɗin Nijeriya ba — Maryam Abacha

Ya ce sauyin da al’umma za su gani a yanzu, ba wai na rage farashin man ba ne kaɗai, wanda zai sauya baki ɗaya yadda ake gudanar da harkokin mai ne a ƙasar.

“A yanzu da shugaban ƙasa ya ziyarcemu, kuma ya ba mu ƙarin makamashi, ina mai shaida muku cewa nan ba da jimawa ba za ku ji daga garemu, kuma zai kasance sauyi ne a ɓangaren mai baki ɗaya a ƙasar, ba wai kawai rage farashinsa ba kaɗai.”

A watan Oktoban bara ne dai Matatar Dangote ta fara saida man fetur, lamarin da ya kawo saukar farashinsa a ƙasar.

To sai dai dillalan man fetur a Nijeriya, na ganin ya kamata Matatar Dangoten ta riƙa saida lita ɗaya ƙasa da Naira ɗari 8, la’akari da cewar ana sayar wa kamfanin ne da ɗanyen mai a kuɗin Naira maimakon dalar Amurka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Matatar Dangote

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan kashe-kashen Benuwe — Atiku

Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar, ya yi Allah-wadai da kashe-kashen mutanen da ake yi a Jihar Benuwe, yana mai bayyana lamarin a matsayin mummunar masifa.

Cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, Atiku ya caccakin gwamnatin Nijeriya da cewa ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan lamarin.

Tinubu ya bayar da umarnin binciken hare-haren Benuwe Iran ta rataye mutumin da ta kama yana yi wa Isra’ila leƙen asiri

Ya nuna damuwa matuƙa kan ci gaba da zubar da jini a jihar Benue, yana mai kira ga gwamnatin tarayya da ta ɗauki matakin gaggawa domin kawo karshen matsalar tsaro da ke addabar yankin.

Atiku ya ce al’ummar Benuwe na fama da hare-hare na tsawon shekaru, inda rayuka ke salwanta, kauyuka ke lalacewa, iyalai ke rasa muhallansu.

“Abin da muke buƙata shi ne samun zaman lafiya da noma ba tare da fargabar mutuwa ba, da kuma bai wa ’ya’yansu tarbiyya cikin kwanciyar hankali,” in ji Atiku.

Ya jaddada cewa wadannan hakkoki ne da Kundin Tsarin Mulki na Kasa ya tanada, kuma wajibi ne gwamnati ta kare su.

Ya kuma yi Allah-wadai da yadda jami’an tsaro ke amfani da karfi da hayaki mai sa hawaye wajen tarwatsa masu zanga-zangar lumana a Benue da ke neman kariya daga gwamnati.

“Wannan ba salon mulki ba ne, illa zalunci ne da cin amanar shugabanci kuma ya nuna yadda gwamnati ta yi biris da kukan jama’a.”

Atiku ya ƙara da cewa matsalar tsaro ba a Benuwe kaɗai take ba, har da jihohin Filato da Zamfara da Kaduna da kuma Taraba, inda jama’a ke fuskantar irin wannan hali.

Ya bukaci shuwagabanni da gwamnatocin jihohi da su mayar da hankali kan kare rayukan ‘yan ƙasa fiye da yin fito na fito da siyasa, ta hanyar aiki da hukumomin tsaro da samar da kayan aiki masu inganci ga yankunan da abin ya shafa.

Hakazalika, Atiku ya yi kira ga ’yan Nijeriya da kada su yi shiru a kan zalunci. Ya bukace su da su ɗaga murya su nemi adalci da ɗaukar mataki.

Tuni dai Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bai wa mahukunta umarnin bincike da gano waɗanda ke da alhakin kai munanan hare-haren da suka janyo salwantar rayukan fiye da mutum 100 a Jihar Benuwe.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jirgin alhazai ya yi saukar gaggawa kan barazanar harin bom
  • Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran
  • Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan sabon harin Iran
  • Mun bankaɗo sabuwar dabarar ’yan siyasa ta satar kuɗi — EFCC
  • Mun bankaɗo sabuwar dabarar ’yan sisaya ta satar kuɗi — EFCC
  • Gwamnati ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan kashe-kashen Benuwe — Atiku
  • Matatar Dangote Za Ta Fara Dakon Man Fetur Da Dizal Kyauta A Fadin Nijeriya
  • Sabon harin Iran ya hallaka mana mutum 8 – Isra’ila
  • Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas
  • Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya