Majiyar sojan Rasha ta sanar da cewa; Tun daga watan Febrairu na 2024, zuwa yanzu ta tarwatsa tankokin yaki samfurin ” Abrams” kirar Amurka da ta bai wa kasar Ukiraniya har guda 26. Ya zuwa yanzu adadin wadannan tankokin da su ka rage a tare da sojojin Ukiraniya ba su wuce 5, ba domin adadinsu 31 ne.

Kamfanin dillancin labarun ” Sputnik” ne ya bayyana cewa; adadin  tankokin yakin  na Amurka da su ka saura a tare da sojojin Ukiraniya ba su wuce 5 ba.

Tun a watan Janairu na 2023 ne dai tsohon shugaban kasar ta Amurka Joe Biden ya sanar da bai wa Ukiraniya  tankokin yaki samfurin Abrams a karkashin taimakon kayan yakin da take bai wa kasar.

Dama dai shugaban hukumar leken asirin kasar Ukiraniya Kyrylo Budanov ya sanar da cewa; Wadannan tankokin na Amurka ba za su iya jurewa a yaki ba, sai idan za a yi amfani da su ne a cikin wasu wurare kadan. 

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Iraki Ta Yi Watsi Da Bukatar Amurka Akan Dakarun Sa Kai Na” Hashdus-sha’abi”

Ofishin Fira ministan kasar Iraki ya fitar da bayani a yau Laraba akan abinda ya gudana a tsakanin Muhammad Shiya al-Sudani da sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio a tattaunawar wayar tarho.

Sakataren harkokin wajen Marco Rubio ne ya kira yi fira ministan Iraki inda su ka tattauna alakar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma halin da ake ciki a wannan yankin.

Sudani ya yi ishara da hare-haren bayan nan da aka kai wa cibiyoyin man fetur dake yankin Kurdistan na Iraki da kuma yankin Salahuddin a Karkuk.

Haka nan kuma ya ce a halin yanzu jami’an tsaro suna gudanar da bincike domin gano wadanda su ka kai harin.”

Haka nan kuma Fira ministan na kasar Iraki ya bayyana mamakinsa akan yadda kai harin ya faru a lokacin da aka kulla yarjejeniya a tsakanin ma’aikatar man fetur din Iraki da kuma kamfanoni masu zuba hannun jari daga Amurka.”

Fira ministan harkokin wajen na Iraki ya kuma yi Magana akan rundunar sa kai ta “Hashdus-sha’abi” yana mai cewa; ana yi wa dokokin tsaron Iraki kwaskwarima ne a gaban majalisar da zai shafi rundunar sa-kai din wacce cibiya ce da Iraki ta amince da ita a gwamnatance.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar
  • Kungiyar “Human Right Watch” Ta Yi Kira Da A Saki Tsohon Shugaban Kasar Nijar Muammad Bazoum
  • Ayatullahi Makarem Shirazi Ya Jinjinawa Al’ummar Iran Kan Hadin kai Da Suka Bayar Lokacin Yakin Kwanaki 12
  • Yan Majalisar Dokokin Kasashen Iran Da Iraki Sun Amince Da Ra’yin Ficewar Sojojin Amurka Daga Iraki
  • Iran Ta Zargi Amurka Da HKI Da Wargaza Dokokin Kasa Da Kasa Da Kuma Yarjeniyoyin Kasa Da Kasa
  • Brazil Ta Shiga Yaki Da HKI, Inda Ta Kudurin Anniyar Goyon bayan Afirka Ta Kudu A Kotun ICJ
  •  Iraki Ta Yi Watsi Da Bukatar Amurka Akan Dakarun Sa Kai Na” Hashdus-sha’abi”
  • Shugaban Amurka Trump Ya Bukaci Gurfanar Da Tsohon Shugaban Amurka Barack Obama A gaban Kuliya
  • Pezeshkian: Tunanin Kawo Karshen Shirin Nukiliyar Iran Ya Yi Kama Da Tabuwa
  • Ministocin Tsaron kasashen Rasha Da JMI Sun Hadu A Birnin Mosco