Kafofin yada labarai daga Isra’ila na tabbatar da kutsen da akayi wa kasar akan wasu takardun bayyanan sirrin shirinta na nukiliya.

Wannan na zuwa ne kwana guda bayan da Iran ta ce ta samu tarin takardun sirri da suka shafi ayyukan nukiliyar Isra’ila.

Ministan leken asirin kasar Iran Esmail Khatib ya ce tarin takardun sirri na Isra’ila da kasar ta samu na da alaka da makaman nukiliyar gwamnatin kuma za su kara karfi ga tsarin garkuwa daga hare-haren sama na Iran.

“Takardun da muka samu na da alaka da bayanai game da cibiyoyin nukiliyar su,” kamar yadda Khatib ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na IRIB.

Kafafen yada labaran Isra’ila sun tabbatar da hakan, tare da bayyana shi a matsayin “babban kutse.”

Ba tare da bayar da karin bayani ba, wadannan majiyoyin sun bayyana cewa “dubban takardu ne da suka shafi tsare-tsare da na’urorin nukiliya na gwamnatin Sahayoniya.”

Saidai ma’aikatar harkokin soji ta Isra’ila ba ta ce uffan ba kan lamarin.

Tashar talabijin ta 12 ta Isra’ila ta tabbatar da cewa Tehran ta yi nasarar samun wasu muhimman bayanai da ke da alaka da shirin nukiliyar Isra’ila,

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

An wajabta wa ɗaliban firamare mallakar lambar NIN a Bauchi

An wajabta wa ɗaliban makarantun firamare da Ƙaramar Sakandare mallakar lambar shaidar zama ɗan ƙasa (NIN) a Jihar Bauchi.

Hukumar Kula da Ilimin Bai-ɗaya a Matakin Farko ta jihar (SUBEB) ce ta bayar da umarnin ta hannun shugabanta, Alhaji Adamu Mohammed Duguri.

Ya bayyana cewa mallakar lambar NIN ta zama tilas lura da duk hukumomin shirya jarabawa da manyan makarantu suna amfani da ita kafin yi wa ɗalibai rajista.

Ya umarci shugabannin makarantun firamare da sakandare da su umarci ɗalibansu da su tabbata sun yi rajistar katin shaidar ɗan ƙasa sun mallaki lambar NIN kafin shekarar da za su zana jarabawar kammala makarantar da suke.

NAJERIYA A YAU: Yadda tsadar taki ke hana noman masara da shinkafa A tsananta hukunci kan masu dukan mata — Sarki Sanusi

Haka zalika ya buƙaci da su tabbatar ’ya’yansu sun mallaki lambar NIN kafin su kai aji 6 na firamare zuwa aji 3 na Ƙaramar Sakandare domin guje wa makara.

Haka kuma ya umarci Sakatarorin Ilimi na ƙananan hukumomin jihar su tabbatar an bi wannan umarni sau da ƙafa domin guje wa fafar hira a ranar tafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Iraki Ta Yi Watsi Da Bukatar Amurka Akan Dakarun Sa Kai Na” Hashdus-sha’abi”
  • Babban Hafsan Sojin Iran Ya Ce: Iran Zata Sanya Duk Wanda Ya Dauki Matakin Wuce Gona Kanta Nadama
  • Pezeshkian: Tunanin Kawo Karshen Shirin Nukiliyar Iran Ya Yi Kama Da Tabuwa
  • Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu
  •  Iran Ta Yi Kira Ga “FIFA” Da Ta Kori “Isra’ila” Daga Cikinta
  • An wajabta wa ɗaliban firamare mallakar lambar NIN a Bauchi
  • MDD Ta Gargaɗi Isra’ila Kan Tilasta Wa Al’ummar Deir al-Balah Na Gaza Tashi
  • Jami’in Shari’ar Kasa Da Kasa Ya Bayyana Cewa: Harin Da Aka kai Kan Iran Babban Laifi Ne
  • Jaridar Washington Post Ta Ce; Yeman Ta Gurguta Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Isra’ila
  • Ministocin Tsaron kasashen Rasha Da JMI Sun Hadu A Birnin Mosco