Rahotanni na tabbatar da babban kutse akan takardun ayyukan nukiliya Isra’ila
Published: 8th, June 2025 GMT
Kafofin yada labarai daga Isra’ila na tabbatar da kutsen da akayi wa kasar akan wasu takardun bayyanan sirrin shirinta na nukiliya.
Wannan na zuwa ne kwana guda bayan da Iran ta ce ta samu tarin takardun sirri da suka shafi ayyukan nukiliyar Isra’ila.
Ministan leken asirin kasar Iran Esmail Khatib ya ce tarin takardun sirri na Isra’ila da kasar ta samu na da alaka da makaman nukiliyar gwamnatin kuma za su kara karfi ga tsarin garkuwa daga hare-haren sama na Iran.
“Takardun da muka samu na da alaka da bayanai game da cibiyoyin nukiliyar su,” kamar yadda Khatib ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na IRIB.
Kafafen yada labaran Isra’ila sun tabbatar da hakan, tare da bayyana shi a matsayin “babban kutse.”
Ba tare da bayar da karin bayani ba, wadannan majiyoyin sun bayyana cewa “dubban takardu ne da suka shafi tsare-tsare da na’urorin nukiliya na gwamnatin Sahayoniya.”
Saidai ma’aikatar harkokin soji ta Isra’ila ba ta ce uffan ba kan lamarin.
Tashar talabijin ta 12 ta Isra’ila ta tabbatar da cewa Tehran ta yi nasarar samun wasu muhimman bayanai da ke da alaka da shirin nukiliyar Isra’ila,
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
HKI Ta Kashe Wani Babban A Cikin Shuwagabannin Falasdinawa
Daya daga cikin shuwagabannin Falasdinawa ya yi shahada sanadiyyar hare-haren da sojojin HKI suka kai kan zirin gaza.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya bayyana cewa Asa’d Abu Sharia shi ne baban sakataren kungiyar ‘Dakarun Palastinewa”. Wacce aka kafa a shekara ta 2001 M.
Kungiyar kanta ta tabbatar da wannan labarin ta kuma bayyana cewa ya dade yana shugabantar wannan kungiyar sannan a ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 ya shiga cikin yakin da aka fara kan HKI kuma dakarunsa sun kama yahudawa da dama suka shigo da su su gaza. Banda haka shi ne yake jagorantar bangaren soje na kungiyarsa. Sau da dama ya jagoranci Falasdinawa a yaki da yahudawan a Gaza. Sannan kungiyar tana da reshe a yankin yamma da kogin Jordan.
A wani labarin kuma kungiyar ta kara da cewa tare da shi akwai dan uwansa Ahmed Abu Sharia, ko wanda akewa Lakabi da Abu Falasteen, sun yi shahada tare. Banda haka kafin shahadarsa Abu Sharia ya rasa danginsa na kusa kimani 150 a yankin tufanul Aksa ya zuwa yanzu.