Iran A Shirye Take Ta Bada Dama A Gudanar Da Bincike A Cibiyoyin Nukliyar Kasar
Published: 8th, June 2025 GMT
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiyan ya bayyana cewa kasar Iran tana gudanar da ayukanta na bincike a cibiyoyin Nukliyar kasar tare amincewa da bincike kuma a bayyana take hakan.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya nakalto shugaban yana fadar haja a jiya Asabar a lokacinda yake ganawa da mataimakin firay minister kuma ministan harkokin wajen kasar Kazakistan Murat Abugaliuly wanda yake ziyarar aiki a nan Tehran.
Shugaban ya kara da cewa tun lokacinda kasar ta fara tache sinadarin Uranium hukumar makamacin Nukliya ta duniya IAEA na sanya ido a ayyukanta, sannan tun lokacin bata bada rahoton cewa shirin nata ba ta zaman lafiya ba.
Daga karshe shugaban ya kara da cewa bayan wannan kuma ba zamu taba amincewa wani ya hanamu hakkin sarrafa makamashin nukliya na zaman lafiya ba. Don haramtawa mutanemmu amfani da wannan fasahar mai muhimmanci a rayuwarsu.
Yace a dai-dai lokacinda Iran tana barin a gudanar da bincike a cikin ayyukanta, ba zata bawa wani damar fayyace makomar al-ummarmi da ra’ayinsa ba, inji shugaban.
Ya kammala da cewa JMI a shirye take ta shiga tattaunawa na hankali a kan shirin na makamashin Nukliya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran
Wakilin dindindin na kasar Sin a MDD ya yi kiran hada karfi da karfe a bangaren kasa da kasa don karfafa tattaunawa domin ganin an yayyafa ruwa ga rikicin Isra’ila da Iran.
Wakilin, Fu Cong ya ce, yayin da rikicin yake-yaken sojoji na Isra’ila da Iran ya shiga kwana na takwas, abin bakin ciki ne ganin yadda lamarin yake janyo asarar rayukan fararen hula da dama tare da lalata kayayyakin aiki a dukkan bangarorin biyu.
Ya kara da cewa, idan har wutar rikicin ta ci gaba da ruruwa, ba kawai bangarorin biyu ne za su tafka babbar asara ba, hatta sauran kasashen yankin lamarin zai yi musu mummunar illa.
Fu Cong, ya fada wa wani taron gaggawa na kwamitin sulhun MDD cewa, matakin da Isra’ila ta dauka ya saba wa dokokin duniya da ka’idojin huldar kasa da kasa, yana kuma kawo cikas ga ‘yancin kai da tsaron kasar Iran, tare da yin kafar ungulu ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin. Kuma ba tare da wata shakka ba, kasar Sin ta yi Allah wadai da hakan. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp