Aminiya:
2025-09-17@23:10:40 GMT

2027: Makomar Shettima a matsayin abokin takarar Tinubu na janyo cece-kuce

Published: 7th, June 2025 GMT

Shugaba Bola Tinubu ya samu goyon bayan manyan jiga-jigan jam’iyyar APC domin sake tsayawa takara a zaɓen 2027, amma sunan Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima bai fito ba yayin tattaunawar lamarin da ya haifar da tambayoyi game da makomarsa a siyasa.

Ko da yake Shettima ya halarci babban taron jam’iyyar APC na ƙasa, inda aka nuna wa Tinubu goyon baya, amma ba a ambaci sunansa ba a wajen taron.

Sabon Rikici: An kashe dan shekara 13 da wasu 3 a Filato Kwamishina ya yi murabus saboda sauya sheƙar Gwamnan Akwa Ibom

Wannan ya sa mutane da dama suka fara tunanin ko zai dawo a matsayin mataimaki ɗan takarar shugaban ƙasa a 2027.

Wasu ’ya’yan jam’iyyar na cewa, goyon bayan Tinubu ba yana nufin goyon bayan Shettima ba.

“Zaɓi ne da ke hannun shugaban ƙasa wanda zai zaɓa mataimakinsa,” in ji Cif Sam Nkire, ɗaya daga cikin jiga-jigan jam’iyyar APC.

“Mataimakin shugaban ƙasa dole ya ci gaba da zama lafiya da mutane domin shugaba ya ci gaba da amincewa da su.”

Akwai damuwa daga ɓangaren Arewa maso Gabas, yankin Shettima, inda wasu ke buƙatar a fito a bayyana matsayin mataimakin shugaban ƙasa kafin lokacin zaɓen.

“Muna buƙatar bayani,” in ji Barrista Abdullahi Jalo.

“Shiru a kan Shettima ba abu ne da za a wuce haka kawai ba, kuma ya cancanci a yi wa yankin bayani.”

Har yanzu dai Jihar Borno ce kaɗai daga Arewa maso Gabas da ta fito fili ta nuna goyon bayan Tinubu da Shettima tare.

Masana siyasa suna cewa tarihin Tinubu na canja mataimaka a lokacin da yake gwamnan Legas, inda ya sauya mataimakin gwamna sau uku na iya sake maimaituwa a matakin ƙasa.

Daraktan Yaɗa Labaran APC, Bala Ibrahim, ya jaddada cewa goyon bayan da aka nuna wa Tinubu ya shafi ofishin shugaban ƙasa gaba ɗaya.

“Idan jam’iyya na goyon bayan shugaban ƙasa, to ba a cire mataimakinsa daga ciki ba, sai dai idan shi ya bayyana hakan da kansa.”

Sai dai rashin hoto ko sunan Shettima a cikin tallace-tallacen kamfen ɗin Tinubu da bayanan jam’iyya yana ƙara jefa shakku a zukatan wasu.

Mutane da dama a Arewa maso Gabas na jin kamar ana ƙoƙarin watsar da su, musamman ganin yadda Arewa maso Yamma ke ci gaba da riƙe manyan muƙamai a gwamnatin yanzu.

Ana sa ran za a gudanar da wani babban taro na APC a Gombe a ranar 16 ga watan Yuni don duba wannan lamari.

Masu ruwa da tsaki za su tattauna kan tikitin 2027 da kuma yiwuwar tabbatar da tikitin Tinubu da Shettima.

Amma har yanzu, tambayoyi kan makomar Shettima ba su samu amsa ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: abokin takara Goyon Baya Siyasa Zaɓen 2027 goyon bayan

এছাড়াও পড়ুন:

ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe

Ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin Jihar Yobe (ALGON) ta karrama Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, da lambar yabo ta karramawa bisa himmar ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ke gudanarwa a faɗin jihar.

Karramawar, wacce aka bayyana a matsayin irinta ta farko a tarihin Jihar Yobe, shugabannin ƙananan hukumomi 17 na jihar suka ba da ita ga gwamna.

Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno

Da yake jawabi, shugaban ƙungiyar ALGON a Jihar Yobe, kuma shugaban ƙaramar hukumar Damaturu, Alhaji Bukar Adamu, ya yaba da yadda Gwamna Buni yake gudanar da harkokin mulki na bai ɗaya. Ya ce nasarorin da aka samu sun haɗa da fannoni na ilimi, noma, kiwon lafiya, kasuwanci, da samar da ababen more rayuwa.

“Babu wani sashe a jihar da aka bari a baya a cikin ayyukan ci gaban da Gwamna Mai Mala Buni ke aiwatarwa,” in ji Adamu.

A nasa martanin, Gwamna Buni, wanda mataimakinsa, Alhaji Idi Barde Gubana, ya wakilta, ya karɓi karramawar a matsayin “hanyar mayar da martani mai ƙarfi” da ke tabbatar da tasirin gwamnatinsa a matakin farko.

Ya kuma yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙarin kai Yobe matsayin jiha da za ta iya gogayya da takwarorinta a fagen ci gaban ƙasa.

Wakilinmu ya ruwaito cewa taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ’yan siyasa daga ciki da wajen jihar, da kuma sarakunan gargajiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
  • Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago