2027: Makomar Shettima a matsayin abokin takarar Tinubu na janyo cece-kuce
Published: 7th, June 2025 GMT
Shugaba Bola Tinubu ya samu goyon bayan manyan jiga-jigan jam’iyyar APC domin sake tsayawa takara a zaɓen 2027, amma sunan Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima bai fito ba yayin tattaunawar lamarin da ya haifar da tambayoyi game da makomarsa a siyasa.
Ko da yake Shettima ya halarci babban taron jam’iyyar APC na ƙasa, inda aka nuna wa Tinubu goyon baya, amma ba a ambaci sunansa ba a wajen taron.
Wannan ya sa mutane da dama suka fara tunanin ko zai dawo a matsayin mataimaki ɗan takarar shugaban ƙasa a 2027.
Wasu ’ya’yan jam’iyyar na cewa, goyon bayan Tinubu ba yana nufin goyon bayan Shettima ba.
“Zaɓi ne da ke hannun shugaban ƙasa wanda zai zaɓa mataimakinsa,” in ji Cif Sam Nkire, ɗaya daga cikin jiga-jigan jam’iyyar APC.
“Mataimakin shugaban ƙasa dole ya ci gaba da zama lafiya da mutane domin shugaba ya ci gaba da amincewa da su.”
Akwai damuwa daga ɓangaren Arewa maso Gabas, yankin Shettima, inda wasu ke buƙatar a fito a bayyana matsayin mataimakin shugaban ƙasa kafin lokacin zaɓen.
“Muna buƙatar bayani,” in ji Barrista Abdullahi Jalo.
“Shiru a kan Shettima ba abu ne da za a wuce haka kawai ba, kuma ya cancanci a yi wa yankin bayani.”
Har yanzu dai Jihar Borno ce kaɗai daga Arewa maso Gabas da ta fito fili ta nuna goyon bayan Tinubu da Shettima tare.
Masana siyasa suna cewa tarihin Tinubu na canja mataimaka a lokacin da yake gwamnan Legas, inda ya sauya mataimakin gwamna sau uku na iya sake maimaituwa a matakin ƙasa.
Daraktan Yaɗa Labaran APC, Bala Ibrahim, ya jaddada cewa goyon bayan da aka nuna wa Tinubu ya shafi ofishin shugaban ƙasa gaba ɗaya.
“Idan jam’iyya na goyon bayan shugaban ƙasa, to ba a cire mataimakinsa daga ciki ba, sai dai idan shi ya bayyana hakan da kansa.”
Sai dai rashin hoto ko sunan Shettima a cikin tallace-tallacen kamfen ɗin Tinubu da bayanan jam’iyya yana ƙara jefa shakku a zukatan wasu.
Mutane da dama a Arewa maso Gabas na jin kamar ana ƙoƙarin watsar da su, musamman ganin yadda Arewa maso Yamma ke ci gaba da riƙe manyan muƙamai a gwamnatin yanzu.
Ana sa ran za a gudanar da wani babban taro na APC a Gombe a ranar 16 ga watan Yuni don duba wannan lamari.
Masu ruwa da tsaki za su tattauna kan tikitin 2027 da kuma yiwuwar tabbatar da tikitin Tinubu da Shettima.
Amma har yanzu, tambayoyi kan makomar Shettima ba su samu amsa ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: abokin takara Goyon Baya Siyasa Zaɓen 2027 goyon bayan
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu ta dakatar da babban taron PDP
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta dakatar da jam’iyyar PDP daga gudanar babban taronta na ƙasa da aka shirya yi a Ibadan, Babban Birnin Jihar Oyo, a watan gobe.
Mai shari’a James Omotosho ne, ya bayar da wannan umarni, yayin da yake yanke hukunci kan wata ƙara da aka shigar domin sanin ko jam’iyyar PDP na da ikon ci gaba da shirya taron da aka tsara gudanarwa a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba.
Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4mWaɗanda suka shigar da ƙarar sun haɗa da Austine Nwachukwu, shugaban PDP na Jihar Imo; Amah Abraham Nnanna, shugaban PDP na Jihar Abiya da Turnah George, sakataren PDP na yankin Kudu maso Kudu.
Waɗanda ake ƙarar sun haɗa da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), PDP, Sakataren Jam’iyyar na Ƙasa, Samuel Anyanwu, Sakataren shirya taruka na jam’iyyar, Umar Bature, Kwamitin Ayyuka na jam’iyyar na Ƙasa (NWC) da Kwamitin Zartarwa na jam’iyyar na Ƙasa (NEC).
Masu shigar da ƙarar sun kasance ’yan tsahin Nyesom Wike ne.
Sun roƙi kotu da ta hana gudanar da taron, inda suka bayyana cewar jam’iyyar ta saɓa wa dokokinta, Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999, da kuma Dokar Zaɓe wajen shirya taron.
Lauyansu ya shaida wa kotu cewa: “Ba a gudanar da taron wakilai a jihohi 14 ba don haka shirin taron ya saɓa wa doka.”
Sai dai PDP ta kare kanta, inda ta ce lamarin na harkokin cikin gidan jam’iyyar ne, don haka bai kamata kotu ta tsoma baki ba.
Jam’iyyar ta zargi masu ƙarar da ƙoƙarin tayar da rikici domin hana ta gudanar da sabon zaɓen shugabanni.
Aminiya ta ruwaito cewa wannan rikici ya ƙara dagula al’amura a jam’iyyar PDP.
Sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, a baya ya yi zargin cewa an yi amfani da hannunsa na bogi a takardun da aka aike wa INEC game da shirya taron.
Amma shugabancin jam’iyyar ya ƙaryata wannan zargi.
A halin yanzu, Kwamitin Shirya Taron na Ƙasa (NCOC) ya ɗage tantance ’yan takara da aka tsara gudanarwa a ranar 28 ga watan Oktoba.
Mutane da dama na ganin ɗage tantance ’yan takarae na da nasaba da jiran sakamakon hukuncin kotu kafin a ci gaba da shirye-shirye.