Aminiya:
2025-07-24@03:56:08 GMT

Ɓarawon waya ya kashe babban jami’in soja da wuƙa a Kaduna

Published: 9th, June 2025 GMT

Wani babban jami’in soja, Laftanar Commodore M. Buba, ya rasa ransa bayan da wani ɓarawon waya ya soka masa wuƙa a ƙirji.

Lamarin ya faru ne a gadar Kawo, lokacin da jami’in ya tsaya domin gyara tayar motarsa da ta fashe yayin da yake kan hanyarsa ta dawowa daga Jaji, inda yake karatu a Makarantar Horas da Sojoji ta Armed Forces Command and Staff College (AFCSC).

Matawalle ya yi wa Gwamna Lawal da wasu tayin shiga APC  Gwamnatin Tarayya na shirin farfaɗo da kamfanin ƙarafa na Ajaokuta

Shaidu sun bayyana cewa yayin da jami’in ke cikin gyara tayar, sai wani mutum ya zo ya buƙaci ya ba shi wayarsa.

Jami’in soja ya ƙi bayar da wayar, inda ɓarawon ya ciro suka ya soka masa a ƙirji.

Wani jami’in sa-kai, Suleiman Dahiru, wanda ya ga abin da ya faru, ya yi ƙoƙarin taimaka masa, amma shi ma ɓarawon ya yanke shi da wuƙa a hannu.

Mutanen da ke kusa da wajen take suka kashe ɓarawon da duka.

An garzaya da jami’in sojan zuwa Asibitin Manaal, amma likitoci suka tabbatar da rasuwarsa.

Daga baya an ɗauki gawarsa zuwa ɗakin ajiye gawarwaki na Asibitin 44 Nigerian Army Reference Hospital da ke Kaduna.

Wani babban jami’in soja da bai so a bayyana sunansa ba, ya ce sojoji da ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro sun shiga cikin gari cikin kaya domin gudanar da bincike da kuma kawar da masu aikata laifuka a Kaduna.

Kakakin rundunar ’yan sandan Kaduna, ASP Mansir Hassan, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana shi a matsayin abin takaici.

Ya kuma tabbatar wa jama’a cewa rundunar ƙoƙarin ƙara tsaurara matakan tsaro a faɗin jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kawo

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Hamas Ta Yi Suka Kan Kame ‘Yan Gwagwarmaya Da Hukumar Falasdinawa Ke Yi

Jami’in kungiyar Hamas ya bayyana cewa: Kamen da hukumar Falasdinawa ta yi wa ‘yan gwagwarmaya a yankin Gabar Yammacin Kogin Jordan yana nuna goyon baya ne ga ‘yan mamayar Isrta’ila

Jami’in kungiyar Hamas Abdel Rahman Shadid ya bayyana cewa: Kamen da jami’an tsaron Hukumar Falasdinawa suka yi na wani gungun ‘yan gwagwarmaya a Nablus da Jenin, da kwace makamansu, da kuma ci gaba da fatattakar ‘yan gwagwarmaya a duk fadin yankin gabar yammacin kogin Jordan, yana nuni da ci gaba da goyon bayan gwamnatin mamayar Isra’ila ce da murkushe al’ummar Falastinu.

A cewar cibiyar yada labaran Falasdinu, Shadid ya jaddada a cikin wata sanarwa da ya fitar cewa: Kamen da jami’an tsaron hukumar cin gashin kan Falasdinawa suka yi kan ‘yan gwagwarmaya da kuma fitattun al’umma da masanan Falasdinawa, biyan ladar moro-maron yahudawan sahayoniyya ne da jami’an hukumar Falasdinu suka ci.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake ruguza gidajen mutane a Jenin, tare da koran dubban mutane a Tulkarm, ana kuma kwace yankunan mutane a gabar yammacin kogin Jordan.

Shadid ya bayyana cewa: Wadannan ayyuka suna nuna manufar Hukumar Cin gashin Falasdinawa ne na ganin ta raba ‘yan gwagwarmaya da yankin gabas yammacin kogin Jordan, tare da barin Falasdinu a bude ga sojojin mamayar Isra’ila gungun ‘yan ta’addan su aiwatar da tsare-tsaren Sanya Falasdinawa gudun hijira.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Uwa ta kashe ’ya’yan cikinta biyu saboda kuncin rayuwa
  • An kone babur din ‘barayin waya’ a Kano
  • Har Yanzu Yaƙi Da Ta’addanci Ne Babban Muradin Gwamnatina — Tinubu
  • Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa
  • Zazzaɓin Lassa ya kashe mutum 151 a Nijeriya bana — NCDC
  • Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh
  • Tsoffin Jami’an ‘Yan Sanda Sun Bukaci A fitar Da Su Daga Cikin Shirin Fansho
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kwara Ta Taimaka Wajen Hana Lalacewar Wani Bene A Ilorin
  • Jami’in Shari’ar Kasa Da Kasa Ya Bayyana Cewa: Harin Da Aka kai Kan Iran Babban Laifi Ne
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Suka Kan Kame ‘Yan Gwagwarmaya Da Hukumar Falasdinawa Ke Yi