Ɓarawon waya ya kashe babban jami’in soja da wuƙa a Kaduna
Published: 9th, June 2025 GMT
Wani babban jami’in soja, Laftanar Commodore M. Buba, ya rasa ransa bayan da wani ɓarawon waya ya soka masa wuƙa a ƙirji.
Lamarin ya faru ne a gadar Kawo, lokacin da jami’in ya tsaya domin gyara tayar motarsa da ta fashe yayin da yake kan hanyarsa ta dawowa daga Jaji, inda yake karatu a Makarantar Horas da Sojoji ta Armed Forces Command and Staff College (AFCSC).
Shaidu sun bayyana cewa yayin da jami’in ke cikin gyara tayar, sai wani mutum ya zo ya buƙaci ya ba shi wayarsa.
Jami’in soja ya ƙi bayar da wayar, inda ɓarawon ya ciro suka ya soka masa a ƙirji.
Wani jami’in sa-kai, Suleiman Dahiru, wanda ya ga abin da ya faru, ya yi ƙoƙarin taimaka masa, amma shi ma ɓarawon ya yanke shi da wuƙa a hannu.
Mutanen da ke kusa da wajen take suka kashe ɓarawon da duka.
An garzaya da jami’in sojan zuwa Asibitin Manaal, amma likitoci suka tabbatar da rasuwarsa.
Daga baya an ɗauki gawarsa zuwa ɗakin ajiye gawarwaki na Asibitin 44 Nigerian Army Reference Hospital da ke Kaduna.
Wani babban jami’in soja da bai so a bayyana sunansa ba, ya ce sojoji da ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro sun shiga cikin gari cikin kaya domin gudanar da bincike da kuma kawar da masu aikata laifuka a Kaduna.
Kakakin rundunar ’yan sandan Kaduna, ASP Mansir Hassan, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana shi a matsayin abin takaici.
Ya kuma tabbatar wa jama’a cewa rundunar ƙoƙarin ƙara tsaurara matakan tsaro a faɗin jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kawo
এছাড়াও পড়ুন:
Magidanci ya shiga hannu kan kashe matarsa mai juna biyu da duka
’Yan Sanda sun kama wani mutum mai suna Mohammed Sani mai shekara 31 da duniya, bisa zargin dukan matarsa Hauwa mai ɗauke da juna biyu, wanda ya zama ajalinta.
Lamarin ya faru ne a gidansu da ke unguwar Banin Hashim da ke Minna, a Jihar Neja.
Sojojin Isra’ila sun kashe mutum 13 a wajen rabon tallafi a Gaza 2027: Makomar Shettima a matsayin abokin takarar Tinubu na janyo cece-kuceHauwa mai shekara 24 a duniya wadda ke ɗauke da cikin wata tara, an same ta a mace a ɗakinsu kwance cikin jini.
Rundunar ’yan sandan ta samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 10:30 na daren ranar 3 ga watan Yuni, 2025.
Jami’an ‘yan sanda daga sashen A Division a Minna sun garzaya gidan.
Sun garzaya da Hauwa asibitin gwamnati da ke Minna, inda likitoci suka tabbatar da mutuwarta.
Haka kuma, likitoci sun tabbatar cewa tana da juna biyu.
Maƙwabtansu sun shaida wa ‘yan sanda cewa ma’auratan suna yawan samun saɓani, kuma suna zargin mijin ne ya yi wa matar dukan tsiya.
Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya ce an kama Mohammed Sani kuma an miƙa shi zuwa sashen binciken manyan laifuka na jihar (SCID) da ke Minna.