Wadanda suka shirya jirgin agaji zuwa Gaza mai suna Madleen sun bada sanarwan cewa HKI kai farmaki kan jirgin a safiyar yau Litinin.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa jami’an tsaron HKI sun kaiwa jirgin Madleen hare-hare a safiyar yau Litinin kafin iasar Jirgin agajin zuwa gabar tekun Medeterania a gaza.

Labarin ya kara da cewa Thiago Avila, dan rajin kare hakkin bil’adama daga kasar Brazil a cikin Jirgin ya bayyana cewa sojojin yahudawan sun yiwa jirgin kofar rago  .  Y ace sojojin ruwa na HKI sun kaiwa jirgin agaji ” Madleen farmakai. Jirgi wanda yake kokarin  keta kofar ragon da HKI ta yi wa Gaza tun shekara 2006.

Labarin ya kara da cewa sojojin yahudawan sun kama masu rajen kare hakkin mutanen Gaza, dake cikin jirgin ruwa na Madleen saboda an daina jinn duriyarsu.

Daga cikin wadanda suke cikin wannan jirgin dai, wadanda kuma suke tsare a hannun jami’an tsaron HKI sun hada da Greta Thunberg mai rajin kare yanayi, sannan mutane 12 wadanda suke rajin kare mutanen Gaza ta hanyar Jirgin Madleen, da kuma

Sai kuma Liam Cunningham da Rima Hassan, yan majalisar dokokin Taarayyar Turai daga kasar faransa kuma yan asalin kasar Falasdinu. Labarin yace LIMA ta yada sautin da karar jiniyar da sojojin yahudawan suka kunna a lokacin kai masu hari.

Kamfanin dillancin labaran AFP na kasar Faransa ya nakalto Mahmood Abu-Odeh dan jarida wanda yake bin jirin ceton na Madleen daga kasar Jamus ya bayyana cewa an kama wadanda suke jirgin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa Kisan Kiyashi A Rannakun Bikin Babbar Salla

A rana ta biyu tabukuwan  babbar salla, sojojin HKI suna ci gaba da yi wa Falasdinawa kisan kiyasahi da kuma rusa matsugunansu a yankin Gaza.

A yau Asabar kadai gwamman Falasdinawa ne su ka yi shahada a cikin sansanonin da Falasdinawa suke gudun hijira a cikinsu.

An sami shahidai 5  da kuma wasu mutane  biyu da su ka jikkata a kusa da cibiyar rana kayan agaji a yammacin Rafah dake kudancin zirin Gaza.

A yammacin birnin Khan-Yunus kuwa wasu Faladinawa 12 ne su ka yi shahada, yayin da wasu 40 su ka jikkata saboda harin da ‘yan sayahoniyar su ka kai wa sansaninsu.

A arewacin Khan-Yunus kuwa, sojojin mamayar sun ruguza gidajen Falasdinawa da dama.

A kusa da cibiyar kiwon lafiya ta ” Majma’u -Shifa” dake yammacin birnin Gaza, adadin shahidai ya kai 7 wasu biyu kuwa su ka jikkata.

Daga lokacin da HKI ta shelanta yaki akan mutanen Gaza a 2023, adadin wadanda su ka yi shahada sun kai 54,677, yayin da wadanda su ka jikkata su ka kai 125,530.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Leken Asiri Na Iran Ya Yi Karin Bayani Kan Nasarar Samun Bayan Tsaron HKI
  • HKI Ta Kaiwa Jirgin Ruwan Masu Rajin Kare Hakkin Mutanen Gaza Na Jinkai
  • Sojojin Amurka Sun Harba Tear Gas Da Albarusan Ruba Kan Masu Zanga-Zanga A Los Angeles a jiya Lahadi
  •  Fiye Da Falasdinawa 90 Ne Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24 Da Su Ka Gabata
  • Jirgin Ruwa “Madeleine” Dake Son Karya Takunkumin Gaza Yana Ci Gaba Da Tafiya
  • Iran: Sabbin Takunkuman Tattalin Arzikin Da Amurka Ta Sake Dorawa Kasar Ya Nuna Kiyayya Ga Iran
  • Sojojin Isra’ila sun kashe mutum 13 a wajen rabon tallafi a Gaza
  • Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa Kisan Kiyashi A Rannakun Bikin Babbar Salla
  • Adadin ‘Yan Jaridar Falasdinu Da Suka Yi Shahada Sun Karu Zuwa 226 Tun Bayan Fara Kisan Kare Dangi A Gaza