Aminiya:
2025-06-12@22:59:34 GMT

Dalilin da babu abin da gwamnatin NNPP ta taɓuka a Kano — APC

Published: 12th, June 2025 GMT

Ƙungiya mai rajin kishin APC a Kano mai suna APC Patriotic Volunteers, ta ce shekaru biyun da jam’iyyar NNPP ta shafe tana mulkin jihar nakasu ne da ke nuna tsantsar rashin ƙwarewarta a gwamnatance.

A taron da ta gudanar da manema labarai a Kano, ƙungiyar bisa jagorancin shugabanta Alhaji Usman Alhaji (Wazirin Gaya) ta ce nazarin da ta yi wa salon mulkin gwamnan jihar Abba Kabir Yusuf, ya tabbatar mata da gazawarsa wajen haɓaka ɓangarori masu muhimmanci duk da makudan kudaden shiga da gwamnatin tarayya ke bata, da kuma kudaden shiga na cikin gida da take samu.

Mokwa: Zulum ya kai ziyarar jaje Neja, ya bayar da tallafin N300m Ana zargin uwa da kashe ’yarta kan Naira 100 a Zariya

“Babu ayyukan a zo a gani idan ka duba biliyoyin da ke shiga jihar.”

Kazalika kungiyar ta zargi gwamnan da wawure Naira biliyan 1.6 da aka ware domin sayen mai da sauran kayan aiki na tsawon watanni uku a ma’aikatar ruwa ta Kano, baya ga gazawa wajen biyan ma’aikata sabon mafi ƙarancin albashi.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Salami: Babu Inda Ba Za Mu Iya Kai Wa Hari Ba A Fadin HKI

Kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran Manjo Janar Hussain Salami ya fada a yau Alhamis cewa; Abokan gaba suna yi mana barazana da yaki, sannan ya tabbatar da cewa a shirye suke su fuskanci duk abinda zai faru.

Manjo janar Salami wanda ya gabatar da jawabi ga taron dakarun sa-kai na “Basiji a nan Tehran ya kuma kara da cewa;  Babu wani wuri komai zurfi da nisansa a HKI da ba mu tsinkayowa, idan kuwa aka ba mu umarni to za su yi nasara, mu Sanya abokin gaba ya yi nadama.

A gefe daya ministan tsaron Iran ya bayyana cewa; Duk wani hari da ake tunanin kawo wa Iran, to kuwa zai fuskanci mayar da martani mai tsanani.

Ministan tsaron na Iran Laftanar janar Azizi Nasri Zadeh ya kara da cewa;  Idan har yaki ya barke, to za a tilasta wa Amruka ficewa daga wannan yankin, kuma asarar da za ta yi sai ta rubanya wacce za ta yi wa Iran.”

Ministan tsaron na Iran ya kuma ce; Abin takaici ne yadda wasu jami’an Amurka su ka yi barazanar yiyuwar barkewar yaki, idan ba a cimma matsaya ba a tattaunawar Nukiliya, sannan ya kara da cewa: Tehran ba ta maraba da yaki, amma kuma a lokaci daya ta shirya masa.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Salami: Babu Inda Ba Za Mu Iya Kai Wa Hari Ba A Fadin HKI
  • Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Afrika
  • Mokwa: Zulum ya kai ziyarar jaje Neja, ya bayar da tallafin N300m
  • Gwamnatin Kano za ta binciki musabbabin gobarar kasuwar Farm Center
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Kogi Ta Gargadi Siyasantar Da Kalubalen Tsaro A Jihar
  • Dalilin da Nijeriya ke fuskantar tsaiko wajen karɓar rancen $5bn daga Saudiyya
  • Sarki Sanusi II Ya Yi Hawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda Na Haramta Hawan Sallah A Kano
  • Gwamnan Jihar California Ya Bayyana Donald Trump A Matsayin Dan Kama-karya