Aminiya:
2025-09-18@05:29:06 GMT

Dalilin da babu abin da gwamnatin NNPP ta taɓuka a Kano — APC

Published: 12th, June 2025 GMT

Ƙungiya mai rajin kishin APC a Kano mai suna APC Patriotic Volunteers, ta ce shekaru biyun da jam’iyyar NNPP ta shafe tana mulkin jihar nakasu ne da ke nuna tsantsar rashin ƙwarewarta a gwamnatance.

A taron da ta gudanar da manema labarai a Kano, ƙungiyar bisa jagorancin shugabanta Alhaji Usman Alhaji (Wazirin Gaya) ta ce nazarin da ta yi wa salon mulkin gwamnan jihar Abba Kabir Yusuf, ya tabbatar mata da gazawarsa wajen haɓaka ɓangarori masu muhimmanci duk da makudan kudaden shiga da gwamnatin tarayya ke bata, da kuma kudaden shiga na cikin gida da take samu.

Mokwa: Zulum ya kai ziyarar jaje Neja, ya bayar da tallafin N300m Ana zargin uwa da kashe ’yarta kan Naira 100 a Zariya

“Babu ayyukan a zo a gani idan ka duba biliyoyin da ke shiga jihar.”

Kazalika kungiyar ta zargi gwamnan da wawure Naira biliyan 1.6 da aka ware domin sayen mai da sauran kayan aiki na tsawon watanni uku a ma’aikatar ruwa ta Kano, baya ga gazawa wajen biyan ma’aikata sabon mafi ƙarancin albashi.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo

Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar SDP a zaben 2023, Adewole Adebayo, ya ce Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ba shi da burin da ya wuce na tara haraji tun yana Gwamna a Legas.

Adebayo ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels.

Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya

A cewarsa, “Kowa ya san cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu sananne ne wajen karbar haraji. Amma wannan tsarin karbar haraji ya fi tsarin da ya tarar da shi wanda ba shi da tsari.

“Ya yi hakan a Legas, sannan ya zo Abuja domin ya dora daga inda ya tsaya a Legas.”

Sai dai Adebayo ya ce Tinubu ya yi kokari wajen bunkasa tattalin arzikin Najeriya.

“A bayyane yake cewa tattalin arzikin da Shugaba Buhari ya bari ba a tafiyar da shi yadda ya kamata ba, kuma yana cikin mawuyacin yanayi kamar na mara lafiya da aka kai dakin jinya. Kamar yadda likita ke bukatar yin cikakken bincike domin gano matsalar mara lafiyan, haka ma ake bukatar fahimtar matsalar tattalin arziki kafin a fara warkar da ita.

“Abin da Shugaba Tinubu ya yi shi ne ya daidaita marar lafiyan, amma ban tabbatar ko ya kai ga gano matsalar ba. Don haka mara lafiyar ba zai mutu nan da nan ba, amma kuma ba a samo maganin cutar shi ba.

“Ba a gano ciwon da ke damun mara lafiyan ba, amma a matsayinsa na likita, yana daukar wasu matakai. Wasu daga cikin matakan ma sun kara ciwon mara lafiyar, amma sannu a hankali likitan yana samun nasara a wasu bangarorin, wanda hakan ke sa wasu su yi tunanin cewa mara lafiyan na kan hanyar warkewa,” in ji Adebayo.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Wadanne Kalubale Gwamna Fubara Zai Fuskanta Bayan Dawowa Mulkin Ribas?
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha
  • Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces