Aminiya:
2025-07-29@09:50:37 GMT

Gini ya kashe Ba’indiye a Zariya

Published: 12th, June 2025 GMT

Wani ɗan ƙasar Indiya, Harpal Singh, ya rasa ransa bayan katangar rumbun ajiya ta kamfanin ATCO da ke Zariya ta rushe a kansa ranar Talata.

Mutumin dai daya ne daga cikin ma’aikatan kamfanin da ke unguwar Cikaji a karamar hukumar Sabon Gari ta jihar Kaduna.

Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai Ana shirin mayar da rantsar da Shugaban Nijeriya zauren majalisa

Wani ma’aikacin kamfanin da ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyanawa Aminiya cewa Ba’indiyen ya gamu da ajalinsa ne da misalin ƙarfe 10:30 na daren Talata, bayan tashin guguwa gabanin a fara ruwan sama.

Ma’aikacin ya ce sai dai ba a san musabbabin rushewar katangar ba, sakamakon lokacin da lamarin ya faru ba lokacin aiki ba ne kuma ba a san abin da ya kai mamacin wurin ba.

Tuni dai aka garzaya da gawar marigayin Harpal ɗakin adana gawarwaki na Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Shika Zariya.

Sai dai wakilin namu ya yi ta ƙokarin tuntuɓar Kakakin Rundunar ’Yan Sandar jihar Kaduna DSP Mansur Hassan kan lamarin, amma wayarsa ba ta shiga.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Zariya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Dashen Itatuwa Na Bana

Gwamnatin Jihar Jigawa ta kaddamar da dashen itatuwa na shekarar 2025 tare da sabunta kudirin farfado da fiye da hekta 5,000 da ta lalace a fadin jihar.

Gwamna Umar Namadi ne ya bayyana haka a wajen bikin kaddamar da shirin da aka gudanar a shatale-tale na Pentagon da ke Dutse babban birnin jihar.

 

Ya bayyana aikin dashen itatuwan a matsayin ɗaya daga cikin alkawuran da gwamnatinsa ta ɗauka domin ci gaban al’umma, inda ya ce gwamnatin sa za ta ci gaba da aiwatar da shirye-shiryen raya muhalli da kare shi.

Ya ce: “Wannan yana da alaƙa da manufofinmu da suka shafi ƙaddamar da tsare-tsare da suka dace da kare muhalli, da ƙarfafa juriya da dorewar muhalli, da kuma inganta rayuwa mai tsafta da dorewa ga al’umma.”

Yayin da yake bayyana muhimmancin shirin, Malam Umar Namadi ya jaddada cewa kalubalen muhalli kamar ambaliya, sahara, sare itatuwa da kuma rashin daidaiton kula da shara na cigaba da barazana ga rayuwar mutane a jihar.

“Wannan barazana na shafar rayuwarmu ta yau da kullum, abincinmu, lafiyarmu, da kuma zaman lafiyar al’ummomi da dama a fadin jihar. Ya zama wajibi mu hada kai domin yaki da duk wani nau’in lalacewar muhalli.” In ji Gwamnan.

Gwamnan wanda Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Bala Ibrahim ya wakilta, ya bayyana cewa ana amfani da shirin ACReSAL wajen farfado da ƙasa ta hanyar dasa itatuwa, da kiyayewa da kuma tsarin noma da gandun daji.

“Yanzu haka, gwamnatin jihar Jigawa ta hanyar shirin ACReSAL na kokarin farfado da hekta 5,000 a wurare 27 a fadin jihar, ta hanyar samar da katanga ta itatuwa, wuraren kiwo da tsarin gandun daji. Mun riga mun fara sauya yanayin da ake ciki ta hanyar wadannan matakan da za a iya auna su.”

Ya kuma bayyana cewa an duba dokoki guda biyar da suka shafi muhalli kuma an miƙa su zuwa majalisar dokoki domin  gyara.

A cewarsa, dokokin da aka duba sun hada da Dokar Gandun Daji, Dokar Hana Kona Daji, Dokar Kiwon Dabbobi da Dokokin Tsafta.

Gwamna Namadi ya kara da cewa domin rage hadarin ambaliya da sarrafa ruwa, gwamnatin jihar ta sayi injina biyu masu iya aiki a ruwa da ƙasa domin kwance hanyoyin koguna da ciyawar Typha ta toshe.

“Baya ga wannan, gwamnati na aikin gina magudanan ruwa a wurare 32 daban-daban domin farfado da yankunan da ambaliya ta shafa. An kuma gina kilomita 130 na katanga a bakin rafuka domin rage ambaliya, kare gonaki da ƙarfafa ƙarfin gwiwar al’ummomin da ke cikin haɗari.”

Gwamnan ya yi gargaɗi mai ƙarfi ga masu sare itatuwa da masu yin gawayi da su daina, ko kuma su fuskanci fushin doka.

“Ina amfani da wannan dama in gargadi duk masu sare itatuwa ba bisa ka’ida ba, da masu yin gawayi da su daina. Kamar yadda muka ambata, mun duba dokokinmu na muhalli kuma mun tanadi hukunci mai tsauri ga duk wanda ya karya wadannan dokoki.”

Rediyon Najeriya ya bayyana cewa, Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Bala Ibrahim ne ya jagoranci dashen itatuwan da kuma raba irin shukar ga ƙananan hukumomi.

Wannan wani bangare ne na tsare-tsaren kare muhalli na jihar, wanda ya haɗa da samar da irin itatuwa mmiliyan biyu da rabi a duk shekara, wayar da kai, da kuma haɗin gwiwa da hukumomin ƙasa da na ƙetare.

 

Usman Muhammad Zaria

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 
  • Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutumin Da Ake Tuhuma Da Safarar Miyagun Kwayoyi
  • Araqchi: Tattaunawar Nukiliya Wani Zabi Ne Mai Muhaimmanci Wanda Ya Karfafa Matsayin Iran A Duniya
  • Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar
  • HOTUNA: Yadda Aisha ta koma gidan Buhari na Kaduna
  •  An Kashe Sojojin HKI 3 A Yankin Khan-Yunus Na Gaza
  • Rashin abinci mai gina jiki ya kashe yara 650 a Katsina — MSF
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Dashen Itatuwa Na Bana
  • Za a ɗauke wuta na tsawon kwanaki 25 a Legas — TCN