Dakarun bangarori biyu na Sudan dake dauki ba dadi, sun zargi juna da kaddamar da hari kan jerin gwanon motocin dake samar da agajin jin kai na Majalisar Dinkin Duniya. Motocin dai sun fuskanci barin wuta ne a daren ranar Litinin a Al-Koma na yankin Darfur ta arewa, lamarin da ya sabbaba rasuwar jami’an ayyukan jin kai biyar, tare da jikkatar wasu da dama.

Wata sanarwar hadin gwiwa da shirin samar da abinci na Majalisar Dinkin Duniya ko WFP, da asusun UNICEF suka fitar a jiya Talata, ta ce motocin ciki har da manya na dakon kayayyaki 15, suna kan hanyarsu ta zuwa birnin El Fasher mai fama da fari, inda za su kai kayayyakin abinci masu gina jiki lokacin da lamarin ya auku. WFP da UNICEF sun yi Allah wadai da aukuwar wannan lamari, suna musu gargadin cewa hari kan tawagar ma’aikatar jin kai ya sabawa dokokin kasa da kasa.

Game da aukuwar wannan lamari, ma’aikatar harkokin wajen Sudan ta zargi rundunar RSF da kaddamar da harin, ta amfani da jirage marasa matuka, tana mai cewa harin ya tarwatsa manyan motocin dakon kaya da dama, da kone wani jirgin aikin ceto, tare da hallaka wasu direbobi, da jami’an tsaro da fararen hula da dama, baya ga wasu da yawa da suka jikkata.

A wata sanarwar ta daban kuma, hukumar samar da agaji da ayyukan jin kai ta Sudan ko SARHO a takaice wadda ke da alaka da rundunar RSF, ta musanta zargin cewa dakarun RSF ne suka kaddamar da harin, tana mai cewa dakarun gwamnati na SAF ne suka kaddamar da harin ta sama kan jerin gwanon motocin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kaddamar da

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun raunata shugaban ISWAP na Najeriya, Albarnawi

A ci gaba da yakin da suke yi da ’yan ta’adda, sojojin Najeriya sun samu nasarar jikkata jagoran kungiyar ISWAP, Abu Moussab Albarnawi a dajin Sambisa.

Bayanai sun nuna sojoji sun sami nasarar ce bayan wani gagarumin harin da suka kai ta sama a wani sabon sansani na ’yan ta’addan da ke dajin Baikee a yankin Sambisa a Jihar Borno.

Dakarun rundunar da ke karkashin Operation KALACHEN WUTA, wanda bangare ne na rundunar sojojin saman Najeriya da ke karkashin rundunar Operation Hadin Kai (OPHK) ne suka kai harin.

Litar fetur za ta iya komawa N1,000 a Najeriya saboda yakin Isra’ila-Iran – Masana Majalisa ta aike wa Tinubu kudurorin dokar haraji domin ya rattaba musu hannu

Majiyoyin sojojin Najeriya da ke rundunar OPHK wanda Manjo Janar Abdulsalam Abubakar ke jagorantar ta ce an aiwatar da wannan aiki ne a dajin inda ’yan ta’addan suke ci gaba da taruwa a sabon sansanin da suka kafa tare da shirya kai hare-hare kan fararen hula da ke kusa, musamman garin Izge.

Majiyar ta ce wannan aikin da Manjo Janar Abdulsalam Abubakar, Kwamandan Rundunar hadin gwiwa ta Arewa maso Gabas a Operation Hadin ke jagoranta, da kuma kwamandan rundunar sojin sama, kwamanda UU Idris, suka shirya a ranar 13 ga watan Yuni 2025 a jere, yadda aka kai hare-hare da dama kan wuraren taruwar ’yan ta’addan, tare da lalata wasu manyan kadarori da kuma kashe manyan kwamandodi na kungiyar ta ISWAP

Kididdigar barnar da majiyoyi suka tabbatar an yi a harin ta tabbatar da cewa kungiyar ta yi mummunar asara.

Wasu majiyoyin leken asiri sun kara tabbatar da cewa fitaccen shugaban kungiyar ISWAP, Abu Moussab Albarnawi, ya samu munanan raunuka a fuskarsa yayin harin ta sama, duk da cewar har yanzu ba a tabbatar da matsayin raunin da ya ji ba.

Nasarar kawar da ’yan ta’addan da kuma wargaza yunkurinsu na sake haduwa ya rage musu karfin fada sannan ya jefa su cikin rudani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba zai yiwu mu bar Khamenei a raye ba — Isra’ila
  • Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho
  • Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja
  • EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
  • Sojoji sun raunata shugaban ISWAP na Najeriya, Albarnawi
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama
  • Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53
  • Iran ta kai hari hedikwatar hukumar leƙen asirin Isra’ila
  • Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu
  • Sarki ya yi barazanar hana yin Musulunci a garinsa bayan dodanni sun kai wa Musulmi hari