Leadership News Hausa:
2025-07-23@23:38:48 GMT

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Published: 8th, June 2025 GMT

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

PPRO ta bayyana cewa binciken farko ya nuna cewa wanda ake zargin yana auren mahaifiyar wanda aka cutar (da sakaya sunanta).

“An bayyana cewa ya yi lalata da yarinyar a lokacin da mahaifiyarta ke barci, yana shiga dakinta kuma yana aikata abubuwan da ba su dace ba a lokuta da dama.

“Wakil ya ce, “Yarinyar na shan wahala amma duk da haka ta kame bakinta sai da lamarin ya ta’azzara sannan ta fada wa makwabta, wanda hakan ya kai ga daukar matakin kama wanda ake zargi da aikata laifin,”

Ya ce a lokacin da ake yi masa tambayoyi an ruwaito wanda ake zargin ya amsa laifinsa.

“An kwashe wanda abin ya rutsa da shi zuwa asibiti domin duba lafiyarsa da kulawa.

“Kwamishanan ‘yansandan Jihar Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu ya bayar da umarnin mika karar zuwa sashen binciken manyan laifuka na jihar domin gudanar da bincike mai zurfi, daga nan kuma za a gurfanar da wanda ake zargin zuwa kotu.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya bayyana a yayin gudanar da taron manema labaru na yau da kullum da aka yi yau Litinin cewa, bana shekara ce ta cika shekaru 50 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Tarayyar Turai EU. Kuma taron kolin kasar Sin da EU karo na 25 na karatowa. Kasar ta Sin tana fatan kungiyar EU za ta yi aiki tare da ita bisa alkibla guda, da cimma matsaya, da kawar da bambance-bambance, da kuma tsara shirin hadin gwiwa tare cikin shekaru 50 masu zuwa.

Bayan cimma yarjejeniya tsakanin Sin da kungiyar EU, shugaban majalisar Tarayyar Turai António Costa da shugabar hukumar Tarayyar Turai Ursula von der Leyen, za su ziyarci kasar Sin a ranar 24 ga watan Yuli. Shugaban kasar Sin Xi Jinping zai gana da shugabannin na EU guda biyu. Kazalika, firaministan kasar Sin Li Qiang, zai jagoranci taron koli na Sin da EU karo na 25 tare da shugabannin kungiyar ta EU guda biyu.

Bugu da kari, wasu jami’an diflomasiyyar Turai sun bayyana cewa, kasar Sin na kokarin yin amfani da damar sake fasalin hukumomi don bikin cika shekaru 80 da kafuwar MDD wajen fadada tasirinta a MDD. A yayin da yake mayar da martani kan wannan batu, Guo Jiakun ya ce, kasar Sin na son yin hadin gwiwa tare da kasashen Turai wajen daukar bikin cika shekaru 80 da kafuwar MDD a matsayin wata dama ta kara karfafa muhimmin matsayin da MDD take da shi, da taka rawar da ta dace a matsayinta na MDD yadda ya kamata, da sanya kwarin gwiwa da karfafa damawa da bangarori daban daban. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa
  • Uwa ta kashe ’ya’yan cikinta biyu saboda kuncin rayuwa
  • Har Yanzu Yaƙi Da Ta’addanci Ne Babban Muradin Gwamnatina — Tinubu
  • Allah Ya Yi Wa Wakilin Sadarwan Bauchi,  Jafaru Ilelah, Rasuwa
  • Pezeshkian: Tunanin Kawo Karshen Shirin Nukiliyar Iran Ya Yi Kama Da Tabuwa
  • UNICEF na zargin Gwamnatin Nijeriya da cin zarafin ƙananan yara
  • Hisbah Ta Lalata Barasa Ta Naira Miliyan 5.8 A Jigawa
  • Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa
  • Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba
  • Manoma A Kaduna Sun Yabawa Irin Masara Na TELA Saboda Juriyarshi Ga Kwari