Kididiga Ta Nuna Yadda Kasar Sin Ke Samun Bunkasar Tattalin Arzikin Teku
Published: 10th, June 2025 GMT
Kididdigar ci gaban tattalin arzikin bangaren tekun kasar Sin, wadda take muhimmin ma’aunin duba ci gaban tattalin arzikin tekun kasar, ta karu da kashi 2.3 bisa dari a bisa mizanin shekara-shekara, inda ta koma zuwa kaso 125.2 a shekarar 2024, lamarin da ya nuna cewa an samu ci gaba mai karfi a fannin teku.
Ma’aikatar albarkatun kasa ce ta fitar da wannan kididdigar a jiya Lahadi albarkacin bikin ranar teku ta duniya.
Bayanai sun nuna cewa, an inganta tsarin sabbin masana’antun bangaren teku na kasar Sin a shekarar 2024, tare da samun ci gaba a fannin fasahar kere-kere. Haka nan, an samu habakar amfani da tattalin arzikin teku da inganta karamin sashen kididdigar da ake yi da kaso 131 cikin dari a shekarar 2024, wadda ke nuna sashen ya karu da kaso 1.8 bisa dari a mizanin shekara-shekara.
Kididdigar ma’aikatar ta kuma nuna cewa, hada-hadar masana’antun bangaren teku masu tasowa da aka samu a bara ta karu da kaso 7.2 bisa dari a mizanin shekara-shekara. Bugu da kari, kamfanonin da ke da alaka da teku sun samu makudan kudi har yuan biliyan 11.4 kwatankwacin dalar Amurka biliyan 1.58 ta hanyar kudin da ake warewa a tsarin mallakar da kamfanoni masu zaman kansu ga gwamnati, watau IPO, wanda hakan ya kai kashi 17 cikin dari na jimillar kudin tsarin IPO na kasar Sin, inda ya kara nuna karfin harkokin kasuwannin hannun jari na bangaren tekun kasar. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: bangaren teku
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma
Sanarwar ta ce: “Ma’aikatar Harkokin Waje na sanar da jama’a cewa, sakamakon rikicin da ke kara kamari tsakanin Isra’ila da Iran, Gwamnatin Tarayya tana shirin karshe na kwaso ‘yan Nijeriya da suka maƙale a wadannan kasashe.
“Saboda haka, ana shawartar dukkanin ‘yan Nijeriya da abin ya shafa da su kiyaye matakan tsaro da kuma tuntubar ofishin jakadanci mafi kusa domin yin rijista da samun karin umarni.”
Baya ga haka, Gwamnatin Tarayya ta sake kira da a dakatar da fada tsakanin Isra’ila da Iran, tare da bukatar bangarorin su rungumi tattaunawa, su mutunta dokokin kare hakkin dan Adam na duniya, kuma su bai wa rayuwar fararen hula muhimmanci.
Ma’aikatar ta jaddada cewa Nijeriya na goyon bayan hanyoyin warware rikici ta hanyar lumana da kuma tallafa wa zaman lafiya a yankuna da duniya baki daya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp