Kididdigar ci gaban tattalin arzikin bangaren tekun kasar Sin, wadda take muhimmin ma’aunin duba ci gaban tattalin arzikin tekun kasar, ta karu da kashi 2.3 bisa dari a bisa mizanin shekara-shekara, inda ta koma zuwa kaso 125.2 a shekarar 2024, lamarin da ya nuna cewa an samu ci gaba mai karfi a fannin teku.

Ma’aikatar albarkatun kasa ce ta fitar da wannan kididdigar a jiya Lahadi albarkacin bikin ranar teku ta duniya.

Bayanai sun nuna cewa, an inganta tsarin sabbin masana’antun bangaren teku na kasar Sin a shekarar 2024, tare da samun ci gaba a fannin fasahar kere-kere. Haka nan, an samu habakar amfani da tattalin arzikin teku da inganta karamin sashen kididdigar da ake yi da kaso 131 cikin dari a shekarar 2024, wadda ke nuna sashen ya karu da kaso 1.8 bisa dari a mizanin shekara-shekara.

Kididdigar ma’aikatar ta kuma nuna cewa, hada-hadar masana’antun bangaren teku masu tasowa da aka samu a bara ta karu da kaso 7.2 bisa dari a mizanin shekara-shekara. Bugu da kari, kamfanonin da ke da alaka da teku sun samu makudan kudi har yuan biliyan 11.4 kwatankwacin dalar Amurka biliyan 1.58 ta hanyar kudin da ake warewa a tsarin mallakar da kamfanoni masu zaman kansu ga gwamnati, watau IPO, wanda hakan ya kai kashi 17 cikin dari na jimillar kudin tsarin IPO na kasar Sin, inda ya kara nuna karfin harkokin kasuwannin hannun jari na bangaren tekun kasar. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: bangaren teku

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanin Mangal ya kori direba kan dauko yara 21 da aka kama a Kogi

An kori direban Kamfanin Simintin Mangal bayan jami’an tsaro sun kama shi da motar kamfanin dauke da yara 21 da ake zargin an yi safarar su ne daga jihohin Arewa.

Gwamnatin jihar ta ce yaran da ke tsakanin shekaru 6 zuwa 17 an kama su ne bisa sahihan bayanan sirri.

Sanawar da Kwamishinan Yada labarai na jihar, Kingsley Fanwo, ya fitar bayan kama yaran a cikin motar ta yi zargin za a yi amfani da su wajen horar da ’yan ta’adda.

Kamfanin ya nesanta kansa daga lamarin, ya ce direban ya karya dokokin aiki, kuma ya jefa al’umma cikin haɗari.

Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta

Babban Manajan sashin kula da mulki na kamfanin, Musa Umar, ya ce ba da izininsa direban da aka kama ya fita da motar ba, domin iya jigilar siminta kaɗai suke yi ba ɗaukar fasinja ko yara ba.

Gwamnatin Kogi ta ce za a mika yaran ga gwamnatocin jihohinsu bayan tantancewa, yayin da duk wanda aka samu da hannu a safarar zai fuskanci shari’a bisa dokokin hana safarar yara da kare haƙƙin yara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife
  • Majalisar Dattawa Ta Bawa Tunubu Damar Kai Sojoji Zuwa Kasar Benin
  • ’Yan jaridar Daily Trust da Trust TV sun lashe kyautar binciken ƙwaƙwaf ta Wole Soyinka ta bana
  • Kamfanin Mangal ya kori direba kan dauko yara 21 da aka kama a Kogi
  • An dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia
  • Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba
  • Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki
  • Zaben 2027: NNPP Ta Sha Alwashin Maye Gurbin Tinubu da Radda
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya ta gaza — Kwankwaso
  • Mutum 5 sun rasu sanadin gobara da faɗa wa rijiya a Kano