Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya
Published: 9th, June 2025 GMT
A yau Lahadi ne shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Myanmar Min Aung Hlaing, sun mikawa juna sakon murnar cika shekaru 75, da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin kasashen biyu.
Shugaba Xi ya yi nuni da cewa, cikin shekaru 75 da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin Sin da Myanmar, bangarorin biyu sun bi ka’idoji 5 na zama tare cikin lumana, da kuma tunanin Bandung, da sada zumunta, da zurfafa hadin gwiwar samun moriyar juna, da nuna goyon baya ga juna kan manyan batutuwan dake shafar moriyarsu, sun kuma kasance abun koyi a fannin sada zumunta tsakanin kasa da kasa.
Ya ce, kasar Sin tana fatan ci gaba da kokari tare da Myanmar, don gaggauta raya hadin gwiwa mai inganci bisa shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”, da aiwatar da kiran raya kasashen duniya, da kiran kiyaye tsaron duniya, da kiran raya al’adun duniya, da kuma sa kaimi ga raya makomar bai daya ta Sin da Myanmar, don kara cin gajiyar al’ummun kasashen biyu baki daya.
A nasa bangare, shugaba Min Aung Hlaing ya ce, Myanmar ta gamu da girgizar kasa mai tsanani, kuma gwamnatin kasar Sin da jama’arta sun samar da gudummawar jin kai cikin hanzari, wanda hakan ya shaida cewa, al’ummun kasashen biyu suna sada zumunta mai zurfi, da nuna goyon baya ga juna. Kazalika, Myanmar tana jinjinawa kasar Sin bisa goyon bayan da take nuna mata, a turbarta ta kokarin neman samun zaman lafiya, da sulhunta kabilunta, da bunkasa tattalin arziki a kasar, kana tana son sa kaimi ga yin hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu a fannoni daban daban, don raya dangantakar abokantaka mai karfi da moriyar juna a tsakaninsu. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Ministan harkokin wajen Sin Wang Yi, ya nanata matsayin Taiwan da jaddada manufar Sin daya tak a duniya yayin tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na Faransa Jean-Noel Barrot a jiya Jumma’a. Ya kuma bayyana adawar Sin da shigar kungiyar tsaro ta NATO cikin harkokin yankin Asiya da Pasifik.
Wang Yi wanda mamba ne na ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS ya nanata cewa, batun da ya shafi Taiwan, batu ne na cikin gidan Sin da ya shafi ’yancin kasar da iko kan yankunanta, wanda ya bambanta da batun kasar Ukraine. Ya ce Sin na daukar amincewa da manufar kasar daya tak da Faransa ta yi da muhimmanci, kuma tana fatan ganin hakan a aikace.
Bugu da kari, ministan ya bayyana fatan Sin na ganin Faransa ta rike matsayin da ya dace da adawa da shigar NATO cikin harkokin Asiya da Pasifik tare da jaddada cewa, ya kamata kasashen biyu su inganta cudanyar bangarori daban daban da kare tsarin ciniki cikin ’yanci da adawa da ayyukan cin zali.
A nasa bangare, Jean-Noel Barrot ya ce Faransa za ta ci gaba da daukar Sin a matsayin kawa kuma abokiyar hulda, da nace wa manufar Sin daya tak tare da sa ran ci gaba da aiwatar da musaya tsakanin manyan jami’ansu da tuntuba ta kut da kut bisa manyan tsare-tsare tsakaninta da Sin. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp