HausaTv:
2025-06-13@09:33:55 GMT

Wagner ta kawo karshe kasantuwarta a Mali bayan fiye da shekaru uku

Published: 8th, June 2025 GMT

Kamfanin sojojin haya na Rasha, Wagner, ya sanar da janyewarsa daga kasar Mali, abin da ya kawo kƙarshen fiye da shekaru uku na ayyukansa a wannan kasa ta Yammacin Afirka.

“Mun taimaka wa ‘yan kishin kasa wajen gina wata rundunar sojoji mai karfi da tsari, wacce za ta iya kare kasarsu.

Dukkan manyan biranen yankin sun koma karkashin ikon mahukuntan da ke da ikon tafiyar da harkoki a kasar,” in ji Wagner.

Kasar Mali, da ke yankin Sahel, ta sha fama da hare-haren ‘yan tawaye tun daga shekarar 2012, kuma sojojin dake mulki a kasar sun nemi taimakon Rasha bayan sun katse dangantaka da Faransa da sauran abokan hulda.

A farkon wannan shekarar, kasashen Mali, Burkina Faso da Nijar, da sojoji sukayi juyin mulki, sun fice daga kungiyar ECOWAS ta Yammacin Afirka, inda suka  kafa wata sabuwar kungiya mai suna AES.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari

Babban baturen ’yan sanda na birnin Ahmedabad da ke ƙasar Indiya ya bayyana cewa, an ciro gawar mutane sama da 200 na fasinjojin jirgin Air India da ya yi hatsari a yau Alhamis.

Babban jami’in ɗan sandan ya bayyana hakan ne a matsayin bayani na baya-bayan nan kan hatsarin jirgin, wanda ya rikito ƙasa jim kadan bayan tashi, kan hanyarsa ta zuwa birnin London na Birtaniya.

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwaman Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya

Shugaban hukumar kula da sufurin jiragen sama na Indiya ya ce jirgin na ɗauke ne da mutum 242, kuma akasarinsu Indiyawa ne.

Fasinjojin jirgin Indiya da yawa sun mutu a hatsarin

A cewar Kamfanin Dillancin Labarai na AP ya ambato shugaban ƴan sanda na birnin Ahmedabad na cewa akwai yiwuwar babu wanda ya tsira da ransa a hatsarin da jirgin sama mallakin kamfanin sufuri na India Air ya faru yau a birnin.

Ya bayyana hakan ne yayin da yake bayani kan hatsarin jirgin da ke kan hanyarsa ta zuwa birnin London na ƙasar Birtaniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi
  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Leroy Sane ya koma Galatasaray
  • De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City
  • An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • Kasashen Iran Masar Da Kuma Omman Sun Gudanar Da Taro A Oslo
  • Tattalin arzikin Nijeriya zai haɓaka cikin shekaru uku masu zuwa — Bankin Duniya
  • Gwamnan Jihar California Ya Bayyana Donald Trump A Matsayin Dan Kama-karya