Tun daga yau Litinin 9 ga watan Yuni, kasar Sin ta fara aiwatar da manufar bai wa ’yan wasu kasashe iznin shiga cikin kasar ba tare da takardar biza ba, ciki har da Saudiyya, da Oman, da Kuwait, da Bahrain. Kawo yanzu, adadin kasashen da kasar Sin ta bai wa jama’arsu izinin shiga cikin kasar ba tare da takardar biza ba, ya habaka zuwa 47.

Tun daga ranar 9 ga watan Yunin shekara ta 2025, zuwa ranar 8 ga watan Yunin shekara ta 2026, mutanen dake da takardar fasfo daga kasashen Saudiyya, da Oman, da Kuwait, da kuma Bahrain, idan suna so su shigo kasar Sin don yin kasuwanci, ko yawon bude ido, ko ziyartar iyalai da abokansu, ko kuma rangadin aiki na kasa da kwanaki 30, babu bukatar su nemi takardar biza na shiga cikin kasar wato “visa”.

Tuni a shekara ta 2018, kasar Sin ta aiwatar da irin wannan manufa ga Hadaddiyar Daular Larabawa da kuma Qatar, al’amarin da ya sa kawo yanzu kasar Sin ta aiwatar da wannan manufa ga dukkan kasashe membobin kungiyar GCC.

Game da wannan batu, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya ce, karuwar yawan kasashen da kasar Sin ta bai wa jama’arsu izinin shiga cikin kasar ba tare da takardar biza ba, ya shaida babbar niyyarta ta fadada bude kofa ga kasashen waje, kana, Sin za ta ci gaba da kyautata manufofin shiga cikin kasar, da kara habaka yawan kasashen da manufar ta shafa, ta yadda baki ’yan kasashen waje za su kara jin dadin kayayyaki, da kasuwanni, gami da hidimomin da aka samar musu a kasar ta Sin, kuma kasashe daban-daban za su more ci gaba tare da kasar Sin bisa hadin-gwiwar da suke yi. (Murtala Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: shiga cikin kasar kasar ba tare da takardar biza kasar Sin ta da takardar

এছাড়াও পড়ুন:

Kyakkyawar Hulda Tsakanin Sin Da Koriya Ta Kudu Na Da Muhimmanci Ga Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankinsu

A yau Talata ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi kira ga Sin da Korea ta Kudu da su daukaka dangantakarsu zuwa matsayi na gaba ta yadda al’ummominsu za su kara amfana da ita da kawo tabbaci ga duniya mai cike da rashin tabbas, yayin da yake taya Lee Jae-myung murnar lashe zaben shugabancin kasar.

Tabbas kyakkayawar alaka tsakanin Sin da Korea ta kudu ta dace da yanayin da duniya ke ciki da muradun al’ummomin kasashen da ma tabbatuwar zaman lafiya a yankinsu da ma duniya baki daya. A matsayinsu na makwabta, wadanda suka shafe shekaru 33 da kulla huldar diplomasiyya, kyakkyawar hulda tsakaninsu na da matukar muhimmanci musamman a irin wannan lokaci da duniya ke cike da hargitse da sauye-sauye da rashin tabbas.

Kamar yadda shugaba Xi ya bayyana, kasashen biyu makwabta ne da ba za a iya raba su ba. Don haka, ci gaban kowacce daga cikinsu, ci gaba ne ga dayar, haka ma akasinsa. Babu wanda yake kin cudanyar kasa da kasa, amma ya kamata, kowacce ’yantacciyar kasa ta kasance mai ra’ayinta na kashin kai da duba moriyarta da na makwabtanta yayin da take hulda da kasashen waje. Tarihi ya nuna yadda daidaituwar al’amura tsakanin bangarorin biyu ke samun tagomashi yayin da rashinsa ke haifar da koma baya. Yayin da Korea ta Kudu ta samu sabon shugaba, fatan ita ce zai jagoranci kasar wajen tsayawa kan ra’ayi na gaskiya da girmamawa da daidaito yayin cudanya da kasar Sin maimakon ba da dama ga masu wani ra’ayi na son kai don amfani da ita da zummar cimma burinsu. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka
  • Adadin Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Kashe A AfirkaTa Kudu Ya Karu Zuwa 49
  • Kasashen Iran Masar Da Kuma Omman Sun Gudanar Da Taro A Oslo
  • Ministan man Fetur na Kasar Iran Yace Amurka Ta Kasa Hana Iran Saida Danyen Man Fetur Na Kasar
  • An Gudanar Da Taron Ministoci Masu Daidaita Ayyukan Da Aka Amince Yayin Taron FOCAC
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Afrika
  • Shugabannin Sin Da Kongo (Brazaville) Sun Aike Da Wasikun Taya Murna Ga Taron Ministocin Kula Da Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC
  • Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna
  • Xi Ya Zanta Da Takwaransa Na Kasar Koriya Ta Kudu  
  • Kyakkyawar Hulda Tsakanin Sin Da Koriya Ta Kudu Na Da Muhimmanci Ga Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankinsu