HausaTv:
2025-07-27@10:29:25 GMT

WHO : har yanzu kyandar biri na da matukar hadari ga duniya

Published: 10th, June 2025 GMT

Shugaban hukumar lafiya ta duniya, Dr. Tedros Ghebreyesus, ya bayyana cewa har yanzu cutar kyandar biri wato Mpox na kasancewa mai matukar hadari a faɗin duniya.

Wannan sanarwa ta biyo bayan taro na hudu da kwamitin gaggawa na kiyaye dokokin harkar lafiya na duniya IHR ya gudanar a ranar 5 ga Yunin 2025, domin nazarin halin da ake ciki game da yaduwar cutar ta Mpox.

Hukumar ta kuma ce duk da cewa an samu ci gaba a wasu kasashe wajen fuskantar cutar, kwamitin ya gargadi shugaban hukumar da cewa lamarin har yanzu babbar barazana ce ga lafiyar jama’a a duniya.

Kwamitin ya danganta wannan da ci gaba da karuwar yawan masu kamuwa da cutar, ciki har da karin wadanda suka kamu da cutar a yankin Yammacin Afirka, da kuma yiyuwar yaduwar cutar ba tare da an gano ta ba a wasu kasashen da ke wajen nahiyar Afirka.

Sanarwar ta kuma ce har yanzu akwai kalubale wajen gudanar da aikin dakile cutar, ciki har da matsaloli a fannin lura da yaduwar cutar da gwaje-gwaje.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Wa Wasu Manyan Jami’anta Karin Girma

“Sauran su ne Lawan Haruna, Opurum Patrick, Agbo James da Georgewill Onwubiko da sauransu.

“Shugaban PSC ya ce su tuna cewa su abokai ne ga kowa, kuma ya kamata a kowane lokaci su yi daidai da abin da ‘yan Nijeriya ke bukata. Ya kuma ba su tabbacin cewa hukumar za ta ci gaba da yin iya kokarinta don ganin an inganta yanayin aikinsu.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 
  • Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
  • Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka
  • Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah
  • Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Wa Wasu Manyan Jami’anta Karin Girma
  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU
  • Iran: Iran Tana Cikin Kasashe Biyar Na Duniya Da Suka Ci Gaba Wajen Kiwon Dabbobi
  • Kwalara: Mutum 13 sun mutu sama da 236 na jinya a Neja
  • Ɓullar Kwalara: Mutum 13 sun mutu sama da 236 na jinya a Neja
  • Asusun Kula Da Kananan Yara Na Majalisar Dinkin Duniya “UNICEF” Ya Yi Gargadi Kan Bala’in Jin Kai A Gaza