HausaTv:
2025-12-08@03:30:20 GMT

WHO : har yanzu kyandar biri na da matukar hadari ga duniya

Published: 10th, June 2025 GMT

Shugaban hukumar lafiya ta duniya, Dr. Tedros Ghebreyesus, ya bayyana cewa har yanzu cutar kyandar biri wato Mpox na kasancewa mai matukar hadari a faɗin duniya.

Wannan sanarwa ta biyo bayan taro na hudu da kwamitin gaggawa na kiyaye dokokin harkar lafiya na duniya IHR ya gudanar a ranar 5 ga Yunin 2025, domin nazarin halin da ake ciki game da yaduwar cutar ta Mpox.

Hukumar ta kuma ce duk da cewa an samu ci gaba a wasu kasashe wajen fuskantar cutar, kwamitin ya gargadi shugaban hukumar da cewa lamarin har yanzu babbar barazana ce ga lafiyar jama’a a duniya.

Kwamitin ya danganta wannan da ci gaba da karuwar yawan masu kamuwa da cutar, ciki har da karin wadanda suka kamu da cutar a yankin Yammacin Afirka, da kuma yiyuwar yaduwar cutar ba tare da an gano ta ba a wasu kasashen da ke wajen nahiyar Afirka.

Sanarwar ta kuma ce har yanzu akwai kalubale wajen gudanar da aikin dakile cutar, ciki har da matsaloli a fannin lura da yaduwar cutar da gwaje-gwaje.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa

Limamin  Juma’ar Tehran Ayatullah Sayyid Ahmad Khatami ya yi Ishara da yadda tsarin tsaron ‘yan sahayoniya ya rushe a yayin yakin kwanaki 12, yana mai kara da cewa; A wancan yakin na kwanaki 12 an murkushe abokan gaba, don haka idan har su ka sake yin wani gigin to za a sake murkushe su.”

Ayatullah Sayyid Ahmad Khatami ya kuma yi Ishara da jawabin jagoran juyin musulunci na bayan nan da a ciki ya bayyana cewa; Trump da Netanyahu suna cikin wahamin cewa Iran ce aka yi galaba a kanta,amma akasin haka ne ya faru, al’ummar Iran ce ta yi nasara akan Amurka da ‘yan sahayoniya a cikin yakin kwankai 12.

Haka nan kuma limamin na Tehran ya kore cewa; Iran ta aike wa da Amurka wasika, ta hanyar wata kasa, yana mai cewa; Ya kamata su kwana da sanin cewa ba ma aika sako ga Amurkawa wadanda suke cin amanar abokansu ma, kuma ba ma yin tattaunawa da su.

Ayatullah Sayyid Ahmad Khatami ya kuma ce; Ba za mu taba tattaunawa da Amurka ba har sai ta sauta halayyarta, domin abinda Trump yake son fada wa duniya shi ne ya tilasawa Iran zama kan teburin tattaunawa,amma abinda muke fada masa shi ne cewa; wadanda ma su ka gabace ka, daga kan Jimmy Carter har zuwa wadanda su ka biyo bayansu, sun mutu da wannan bakin cikin, kai ma tabbas da wannan bakin cikin za ka shiga kabari.

Ayatullah Sayyid Ahmad Khatami ya kuma ce; Tun tuni jigon da wannan juyin yake bayarsa shi ne cewa; Za ,mu yi yaki, mu kuma mutu,amma ba za mu mika kai ga kaskanci ba.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Da Pakisatan Sun Amince Da Farfado da Layin Dogo Tsakanin Istambul, Tehran Zuwa Islamabad December 5, 2025 Iran Ta Raya Ranar Haramta Takunkuman Bangare Guda A Duniya December 5, 2025 Trump Ya Yabawa Rwanda Da Kongo DMK Kan Sulhuntawa A Yakin Gabancin Kongo December 5, 2025 Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu December 5, 2025 Shin Ziyarar Putin a Indiya alama ce da ke nuna cewa New Delhi na yin watsi da gargadin Trump? December 5, 2025 Iran Ta Mayar Da Martani Kan Sanarwar Bayan Taron  Majalisar Kasashen Yankin Tekun Fasha December 5, 2025 Afirka ta Kudu Za Ta Dauki Hutu Daga Halartar Tarukan G20 A Karkashin Shugabancin Trump December 5, 2025 Microsoft Za Ta Fuskanci Hukunci Kan Taimaka Wa Laifukan Isra’ila A Kan Falasdinawa December 5, 2025 Amurka Tana Sake Yin Bitar Alakar Da Ke Tsakaninta Da Tanzania December 5, 2025 Fadlallah Na Hizbullah Ya Yi Kiran Hadin Kai A Tsakanin Musulmi Da Larabawa Domin Fuskantar Kalubale December 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja
  • Mutum 5 sun rasu sanadin gobara da faɗa wa rijiya a Kano
  • Fadar Shugaban Kasar Benin ta ce Har Yanzu Talon Ne a Kan Mulki
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168
  • Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167
  •   Qatar Tayi Gargardi Game Da Gakiyar Yarjejeniyar Gaza Matukar Isra’ila Bata Janye Ba
  • Nakiya ta hallaka yara 4 a Borno
  • Kwastam ta kama jirgin ruwan Brazil ɗauke da hodar iblis a Legas
  • Yan Sanda Sun Kama Muhuyi Magaji, Tsohon Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci a Kano
  • Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa