Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Aniyarta Ta Ci Gaba Da Tace Sinadarin Uranium
Published: 10th, June 2025 GMT
Iran ta bayyana cewa: Tace sinadarin Uranium wani bangare ne na bunkasa masana’antar nukiliya kuma ba zata amince kan tattaunawa ko yin sulhu kansa ba
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya bayyana cewa: Sarrafa sinadarin Uranium wani bangare ne na masana’antar nukiliya, kuma batu ne da ba za a tattaunawa kansa ko yin sulhu kansa ba, kasancewarsa masana’antar cikin gida ne kuma an shefe tsawon shekaru da dama ana sarrafa shi a cikin kasa, sakamakon kokarin da masana kimiyya suka yi.
A cikin taron manema labarai na mako-mako, Baqa’i ya yi ishara da abubuwan da ke faruwa a duniya a halin yanzu, yana mai jaddada cewa: “abin da ba za a yi watsi da shi ba shi ne halin da ake ciki mai radadi a Falastinu da aka mamaye,” yana mai cewa: Ana ci gaba da “aiwatar da kisan kare dangi a Gaza da Yammacin Gabar Kogin Jordan a daidai lokacin da kungiyoyin kasa da kasa suka yi shiru.”
Ya jaddada cewa, amfani da veto da Amurka ta yi a kan wani kuduri na neman kawo karshen kisan kare dangi a Gaza, lamari ne da ke jaddada goyon bayan Amurka da taimakonta ga gwamnatin yahudawan sahayaoniyya.
Kakakin ya yi ishara da shahadar fararen hula sama da 150 da ba su ji ba ba su gani ba a ‘yan kwanakin nan, yana mai jaddada cewa; “Dole ne kasashen duniya su dauki kwararan matakai don kawo karshen wannan bala’i na jin kai.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Jihar California Ya Bayyana Donald Trump A Matsayin Dan Kama-karya
Ma’aikatar tsaron ta Amurka ta sanar da cewa za ta baza zaratan sojojin kasar na “Marines” akan titunan birnin Los Angeles domin fuskantar tashe-tashen hankulan da ake yi domin hana korar ‘yan ci-rani ba bisa ka’ida ba.
Sanarwar ma’aikata tsaron kasar ta ce; Tuni na shirya sojojin na “Marines” 700 domin su yi aikli da rundunar “National Guards” wacce tuni tana kan titunan birnin bisa umarnin shugaba Donald Trump domin kama ‘yan hijira ba bisa ka’ida ba.
Ministan tsaron kasar ta Amurka ya ce ; za a kai sojojin ne a cikin birnin saboda bayar da kariya ga muhimman gine-ginen gwamnatin tarayya da kuma dawo da doka da oda.
Shugaban kasar ta Amurka Donald Trump ya fada a jiya cewa, ba manufarsa ganin yakin basasa ya barke a Amurka ba, amma kuma ya yi wa masu tayar da kayar baya a cikin birnin Los Angeles barazanar dandana kudarsu saboda yadda suke cutar da rundunar kasa ( National Guards.)
A gefe daya gwamnan Jahar ta California Gavin Christopher dan jam’iyyar Democrat ya yi suka da kakkausar murya akan Shirin aikewa da zaratan sojojin na Amurka akan titunan birnin Los Angelos, yana mai cewa bai kamata a kai sojoji a cikin titunan Amurka ba.
Gwamnan ya kara da cewa; Aikewa da sojoji zuwa titunan California, wani kokari ne na Trump domin kara raba kan al’ummar kasar.”