Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2
Published: 6th, June 2025 GMT
Idan za a tuna dai kamfanonin samar da wutar lantarki a kwanakin baya sun gargadi gwamnatin tarayya kan ci gaba da rike musu basuka wanda yanzu ke neman kai wa naira tiriliyan 4.
A kwanakin baya ne kwamitin majalisar datawa mai kula da wutar lantarki ya nuna damuwarsa kan matsalar karancin wutar lantarki da ta dabaibaye bangaren wutar lantarki, inda ya koka da yadda karancin kudin wutar lantarki a masana’antar, ya nuna cewa gwamnati na rike da kudaden kamfanonin da ke samar da wutar lantarki kusan naira biliyan 200 a duk wata.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: wutar lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu na ƙaddamar da wasu ayyuka a Jihar Kaduna
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu na ziyarar aiki a cikin Jihar Kaduna.
Shugaba Tinubu na ziyarar ne domin ƙaddamar da wasu ayyuka da gwamnan jihar, Uba Sani ya aiwatar a tsawon shekara biyu da ya yi yana mulkin jihar.
Za a dawo da dukkan Alhazai gida ranar 28 ga Yuni – NAHCON Kotu ta ba da belin Natasha kan N50m kan zargin bata sunan AkpabioWasu daga cikin ayyukan da shugaban ya ƙaddamar sun haɗa da: asibitin ƙwararru mai gadaje 300 da gwamnatin jihar ta gina don bunƙasa harkokin lafiya.
Daga nan kuma shugaban ya ƙaddamar da cibiyar koyar da sana’o’i, da kuma motocin sufuri masu amfani da iskar gas ta CNG guda 100.
A cikin waɗanda suka yi wa Shugaba Tinubu rakiya sun haɗa da: Mataikamin Shugaban ƙasa na musamman kan harkokin siyasa, Sanata Ibrahim Masara, da mai taimaka wa shugaban kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu da Shugaban Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau I. Jibrin da wasu manyan jami’an gwamnati.