Yadda Sanusi II da Aminu Ado suka yi sallar Idi daban-daban a Kano
Published: 7th, June 2025 GMT
A ranar Juma’a, al’ummar Musulmi a Jihar Kano suka yi bikin sallah babba tare da sauran Musulmai a faɗin duniya.
Amma a Kano, bukukuwan na bana sun kasance wani iri daban, yayin da sarakuna biyu; Aminu Ado Bayero da Muhammadu Sanusi II suka jagoranci sallar Idi a wurare mabanbanta, lamarin da ke nuna yadda rikicin masarautar Kano ke ƙara ƙamari.
Aminu Ado Bayero, wanda aka sauke daga kan sarauta, ya yi sallar idi a fadar Nassarawa.
Malam Kamalu Inuwa, Sarkin Malamai ne, ya ja sallar, inda ya yi wa’azi kan muhimmancin koyi da Annabi Ibrahim wajen nuna sadaukarwa, haƙuri, da ƙauna.
A lokaci guda, Muhammadu Sanusi II, wanda Gwamnatin Jihar Kano ta dawo da shi kan kujerar sarautar, ya ja sallar Idi a filin Idi na Kofar Mata.
Manyan jami’an gwamnatin jihar sun raka shi, ciki har da mataimakin gwamnan jihar, kwamishinoni, da hakimai.
Bayan sallar, Sanusi ya yi kira ga al’ummar Kano da su taimaka wa hukumomin tsaro wajen yaƙi da rashin tsaro da ƙaruwar tashin hankali a tsakanin matasa, musamman matsalar faɗan daba da ke addabar wasu yankuna a jihar.
Ya kuma yi nuni da muhimmancin tarbiyyar yara daga gida, inda ya bayyana cewar iyaye su ɗauki nauyin tarbiyya domin ganin yaransu sun girma cikin kyawawan ɗabi’u.
Duk da cewa an gudanar da sallar idi a wurare daban-daban, bikin ya gudana cikin kwanciyar hankali a faɗin birnin Kano.
Jami’an tsaro sun kasance a manyan filayen salla domin tabbatar da tsaro.
Wannan sabon salo na gudanar da sallar Idi yana nuna yadda rikicin masarautar Kano ke ƙara tsananta, yayin da kowane daga cikin Sanusi da Aminu ke ci gaba da iƙirarin shi ne Sarkin Kano na gaskiya, yayik da rikicin siyasa da shari’a ke ci gaba da gudana.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Aminu Ado Bayero Bukukuwa sallar Idi a
এছাড়াও পড়ুন:
IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya
Babban dakaktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta Duniya ya tabbatar da cewa Iran ba ta kera makaman nukiliya ba, yana mai jaddada cewa tana ci gaba da kasancewa cikin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya (NPT).
Rafael Grossi, ya shaida wa manema labarai a hedikwatar Majalisar Dinkin Duniya da ke New York cewa “Zan iya cewa babu wani shirin makamin nukiliya domin mun dade muna duba shi.
Wannan ya zo ne yayin da Iran ta yi gargadin cewa aiwatar da abin da ake kira “snapback” da sake sanya takunkumin Majalisar Dinkin Duniya da kasashen Turai uku za su soke yarjejeniyar da ta yi da IAEA kan sake fara hadin gwiwa da aka sanya wa hannu a birnin Alkahira a ranar 9 ga Satumba.
Wannan ya zo ne bayan da Majalisar Dokokin Iran ta amince da doka da ta bukaci gwamnati ta dakatar da duk wani hadin gwiwa da IAEA bayan harin Isra’ila da Amurka a watan Yuni.
A bisa dokar Majalisar Dokoki, ba za a ba wa masu sa ido na IAEA izinin shiga Iran ba sai an tabbatar da tsaron cibiyoyin nukiliya na kasar da na ayyukan nukiliya na zaman lafiya, wanda hakan zai kasance ƙarƙashin amincewar Majalisar Koli ta Tsaron Ƙasa ta Iran.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza November 2, 2025 Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran November 2, 2025 Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania November 1, 2025 Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci