Aminiya:
2025-07-25@02:15:04 GMT

Yadda Sanusi II da Aminu Ado suka yi sallar Idi daban-daban a Kano

Published: 7th, June 2025 GMT

A ranar Juma’a, al’ummar Musulmi a Jihar Kano suka yi bikin sallah babba tare da sauran Musulmai a faɗin duniya.

Amma a Kano, bukukuwan na bana sun kasance wani iri daban, yayin da sarakuna biyu; Aminu Ado Bayero da Muhammadu Sanusi II suka jagoranci sallar Idi a wurare mabanbanta, lamarin da ke nuna yadda rikicin masarautar Kano ke ƙara ƙamari.

Sojoji sun kashe manyan Kwamandojin ISWAP 3 a Borno Kwamishina ya yi murabus saboda sauya sheƙar Gwamnan Akwa Ibom

Aminu Ado Bayero, wanda aka sauke daga kan sarauta, ya yi sallar idi a fadar Nassarawa.

Malam Kamalu Inuwa, Sarkin Malamai ne, ya ja sallar, inda ya yi wa’azi kan muhimmancin koyi da Annabi Ibrahim wajen nuna sadaukarwa, haƙuri, da ƙauna.

A lokaci guda, Muhammadu Sanusi II, wanda Gwamnatin Jihar Kano ta dawo da shi kan kujerar sarautar, ya ja sallar Idi a filin Idi na Kofar Mata.

Manyan jami’an gwamnatin jihar sun raka shi, ciki har da mataimakin gwamnan jihar, kwamishinoni, da hakimai.

Bayan sallar, Sanusi ya yi kira ga al’ummar Kano da su taimaka wa hukumomin tsaro wajen yaƙi da rashin tsaro da ƙaruwar tashin hankali a tsakanin matasa, musamman matsalar faɗan daba da ke addabar wasu yankuna a jihar.

Ya kuma yi nuni da muhimmancin tarbiyyar yara daga gida, inda ya bayyana cewar iyaye su ɗauki nauyin tarbiyya domin ganin yaransu sun girma cikin kyawawan ɗabi’u.

Duk da cewa an gudanar da sallar idi a wurare daban-daban, bikin ya gudana cikin kwanciyar hankali a faɗin birnin Kano.

Jami’an tsaro sun kasance a manyan filayen salla domin tabbatar da tsaro.

Wannan sabon salo na gudanar da sallar Idi yana nuna yadda rikicin masarautar Kano ke ƙara tsananta, yayin da kowane daga cikin Sanusi da Aminu ke ci gaba da iƙirarin shi ne Sarkin Kano na gaskiya, yayik da rikicin siyasa da shari’a ke ci gaba da gudana.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Aminu Ado Bayero Bukukuwa sallar Idi a

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Ta ce: “Kotu ba ta bayar da umarni ba? Ba ku da ikon karɓe fasfona.”

Ba a bayyana wata hujja ko dalili a hukumance ba kan dalilin karɓe fasfo ɗin nata ba, lamarin da ya sa wasu suka zargi cewa ana shirya mata maƙarƙashiya irin ta siyasa.

An hangi mijinta, Cif Uduaghan, yana kiran waya cikin sauri yayin da lamarin ya ɗauki lokaci.

Bayan ‘yan mintuna, jami’an sun mayar mata da fasfo ɗin ba tare da wani bayani ba.

An bar ta ta shiga jirgin kafin ya tashi.

Wasu daga cikin fasinjojin da suka shaida lamarin sun bayyana abin a matsayin abin kunya, inda suke kallon lamarin a matsayin amfani da ƙarfi ba bisa ƙa’ida ba.

Har yanzu, hukumar shige da fice ta ƙasa da ofishin Shugaban Majalisar Dattawa ba su ce komai ba game da lamarin ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU
  • Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
  • Ruwa da iska sun kashe mutum 5, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
  • Ruwa da iska sun kashe mutum, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 11 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Sakkwato
  • An kone babur din ‘barayin waya’ a Kano
  • Sheikh Qasem: Nuna Halin Ko In-Kula Na Duniya Ne Ya Jawo Kisan Kiyashi A Gaza
  • Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa
  • A binciko mesar da ta ɓace a Kano — Sanusi II
  • A tsananta hukunci kan masu dukan mata — Sarki Sanusi