Aminiya:
2025-09-18@00:00:52 GMT

Yadda Sanusi II da Aminu Ado suka yi sallar Idi daban-daban a Kano

Published: 7th, June 2025 GMT

A ranar Juma’a, al’ummar Musulmi a Jihar Kano suka yi bikin sallah babba tare da sauran Musulmai a faɗin duniya.

Amma a Kano, bukukuwan na bana sun kasance wani iri daban, yayin da sarakuna biyu; Aminu Ado Bayero da Muhammadu Sanusi II suka jagoranci sallar Idi a wurare mabanbanta, lamarin da ke nuna yadda rikicin masarautar Kano ke ƙara ƙamari.

Sojoji sun kashe manyan Kwamandojin ISWAP 3 a Borno Kwamishina ya yi murabus saboda sauya sheƙar Gwamnan Akwa Ibom

Aminu Ado Bayero, wanda aka sauke daga kan sarauta, ya yi sallar idi a fadar Nassarawa.

Malam Kamalu Inuwa, Sarkin Malamai ne, ya ja sallar, inda ya yi wa’azi kan muhimmancin koyi da Annabi Ibrahim wajen nuna sadaukarwa, haƙuri, da ƙauna.

A lokaci guda, Muhammadu Sanusi II, wanda Gwamnatin Jihar Kano ta dawo da shi kan kujerar sarautar, ya ja sallar Idi a filin Idi na Kofar Mata.

Manyan jami’an gwamnatin jihar sun raka shi, ciki har da mataimakin gwamnan jihar, kwamishinoni, da hakimai.

Bayan sallar, Sanusi ya yi kira ga al’ummar Kano da su taimaka wa hukumomin tsaro wajen yaƙi da rashin tsaro da ƙaruwar tashin hankali a tsakanin matasa, musamman matsalar faɗan daba da ke addabar wasu yankuna a jihar.

Ya kuma yi nuni da muhimmancin tarbiyyar yara daga gida, inda ya bayyana cewar iyaye su ɗauki nauyin tarbiyya domin ganin yaransu sun girma cikin kyawawan ɗabi’u.

Duk da cewa an gudanar da sallar idi a wurare daban-daban, bikin ya gudana cikin kwanciyar hankali a faɗin birnin Kano.

Jami’an tsaro sun kasance a manyan filayen salla domin tabbatar da tsaro.

Wannan sabon salo na gudanar da sallar Idi yana nuna yadda rikicin masarautar Kano ke ƙara tsananta, yayin da kowane daga cikin Sanusi da Aminu ke ci gaba da iƙirarin shi ne Sarkin Kano na gaskiya, yayik da rikicin siyasa da shari’a ke ci gaba da gudana.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Aminu Ado Bayero Bukukuwa sallar Idi a

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya

A daidaikun kasuwannin Abuja da wasu manyan birane na ƙasar nan, an bayyana yadda farashin doya ke ƙara hawa fiye da yadda ake tsammani.

 

Wannan na faruwa ne duk da cewa yanzu sabuwar doya ta fara shigowa kasuwa, bisa al’ada, a duk shekara fitowar sabuwar doya kan karya farashin wanda yake kasuwa. Sai dai a bana, wasu daililai na sa farashin doya kara hawa.

NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

wannan shine batun da shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba akai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa
  • Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki