Ministan Leken Asiri Na Iran Ya Yi Karin Bayani Kan Nasarar Samun Bayanan Tsaron HKI
Published: 9th, June 2025 GMT
Ministan leken asiri na kasar Iran ya ce asiran tsaron HKI da suka shiga hannun ma’aikatansa sun shafi makaman nukliya na HKI kuma sun nuna kwarewar da jami’an leken asirin kasar suke da shi.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa wannan bayanan zasu taimakawa sojojin JMI wajen sanin wuraren da zasu kai hare hare a duk lokacinda yake ya barke tsakanin Iran da haramtacciyar kasar, na makamai da kuma na yanar gizo.
Labarin ya kara da cewa da jami’an ma’aikatar hukumar leken asiri suka yi kama daga daukar ma’aikatan da suka dace da yin hakan da dabar barun da suke yi amfani da su don kaiwa da bayan da suke bukata ya nuna irin koreawarsu a wannan aikin.
Sannan daga cikin muhimman bayanan da suka samu sun hada da na makaman nukliyar haramtacciyar kasar da kuma dangantakanta da Amurka da kuma kasashen turai rawar da wadan nan kasashe suka taka a karfafa HKI kan makamanta na kissan kaere dangi.
Ministan ya kammala da cewa bayanan da muka samu suna da muhimmanci haka ma hanyar da muka bi muka kai ga bayanan suna da muhimmanci.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Iran Ba Zata Bar Tace Sinadarin Uranium Ba
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Iran ba za ta iya watsi da shirinta na inganta sinadarin Uranium ba
Ministan harkokin wajen na Iran ya fada a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Fox News cewa: Har yanzu ba a dakatar da inganta sinadarin Uranium ba a Iran, duk da irin barnar da aka mata bayan hare-haren da Amurka ta yi mata mai tsanani.
A cikin wata hira da gidan talabijin na Fox News, Araqchi ya ce, “Shin shirin inganta sinadarin Uranium a Iran ya dawo? Shin har yanzu wannan shirin yana ci gaba, ko kuwa barnar da aka yi ta yi tsanani har ta kai ga dakatar da shi gaba daya?” Ya ce: “Ba a dakatar da shi ba, duk da cewa barnar ta yi muni da yawa, amma ba shakka ba za a iya yin watsi da Shirin inganta sinadarin Uranium ba, domin wannan nasara ce ta masana kimiyyar Iran, kuma a halin yanzu abin alfahari ne ga kasar, kuma inganta sinadarin Uranium yana da matukar muhimmanci a gare ta.”
Ministan harkokin wajen na Iran ya kara da cewa: “Iran ba zata taba matsawa wajen inganta sinadarin uranium da kashi 90 cikin dari ba. Iran ta himmatu wajen tabbatar da samar da makamashin Uranium kasa da kashi 5% domin samar da makamashin nukiliya. Kuma tana inganta sinadarin na Uranium zuwa kashi 20% saboda tana da injin binciken TRR.”