Aminiya:
2025-07-25@04:39:05 GMT

Bom ya kashe masu yawon murnar sallah a Sakkwato

Published: 10th, June 2025 GMT

Kimanin mutum bakwai sun riga mu gidan gaskiya bayan tarwatsewar wani abun fashewa da ake zargi mayaƙan Lakurawa sun dasa a Ƙaramar Hukumar Tangaza ta Jihar Sakkwato.

Aminiya ta ruwaito cewa waɗanda lamarin ya rutsa da su da ke kan babura na hanyarsu ta dawowa daga yawon bikin sallah a ƙauyen Gwabro.

Isra’ila ta ƙwace jirgin ruwa a hanyar kai agaji Gaza Sojoji sun kashe wani kwamandan ’yan ta’adda a Yobe

Bayanai sun ce an dasa abun fashewar ne a ƙarƙashin wata itaciya da ke zaman wurin hutawar dakarun sojoji a lokacin da suka fito sintiri a yankin.

Majiyiyo sun ce mutum shida sun mutu nan take yayin da ɗaya daga cikin wasu mata biyu yara da suka jikkata ta rasu washegari.

Mataimakin Shugaban Karamar Hukumar Tangaza, Alhaji Ghazzali Rakah ya tabbatar da faruwar lamarin yana mai cewa waɗanda abin ya shafa mazauna ƙauyen Zurmuku ne.

Wannan dai ba shi na farau ba, domin kuwa a watannin da suka gabata sojoji da dama sun rasu sakamakon tashin abin fashewa a karamar hukumar.

Har yanzu dai matsalar tsaro babbar damuwa ce a wasu sassan Jihar Sakkwato, inda mazauna ke ci gaba da kiran mahukunta da su ƙara jajircewa wajen daƙile ta’adar masu tayar da ƙayar baya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babbar Sallah Jihar Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh

Kimanin mutum 16 sun rasa rayukansu a ranar Litinin bayan wani jirgin rundunar sojin sama ta Bangladesh ya fadi a cikin harabar wata makaranta a Dhaka, babban birnin kasar.

Haɗarin jirgin saman yaƙin ya kuma yi sanadin jikkatar gommai, wanda ya kasance guda daga cikin haɗɗura masu muni da ƙasar ta gani a baya-bayan nan a fannin jiragen sama.

Jihohin da za a samu ruwan sama da iska mai ƙarfi a sassan Nijeriya — NiMet Ƙalubalen da ke tattare da sauya sunan jami’a

Wani mai daukar hoto na kamfanin dillancin labarai na AFP da ke wurin ya ce ya ga jami’an kashe gobara suna kwasar daliban da suka jikkata yayin da sojoji ke taimakawa wajen zakulo mutane daga cikin baraguzan jirgin da ya fadi.

Fiye da mutane 100 ne suka jikkata a hadarin, inda akalla 83 ke karbar magani a asibitoci daban-daban, in ji wani jami’i a ofishin gwamnatin kasar, Muhammad Yunus.

Bayanai sun nuna cewa waɗanda suka jikkata mafi yawansu ɗalibai na karɓar kulawar likitoci, yayinda wasu yayi munin da sai anyi musu gagarumar tiyatar sauya hallita.

Jirgin na F-7 BJI da aka kera a kasar Sin ya tashi ne da karfe 1:06 na rana (07:06 GMT) kuma ya faɗi mintuna kaɗan bayan da aka saki ɗaliban daga ajujuwansu don fita tara a harabar makarantar mai suna Milestone School and College.

Faya-fayan bidiyo sun nuna yadda iyayen ɗaliban suka isa filin makarantar a ƙiɗime, don neman yaransu, amma wasu anan suka ci karo da gawargwakin yaransu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ruwa da iska sun kashe mutum 5, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
  • Ruwa da iska sun kashe mutum, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka sace
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 11 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Sakkwato
  • Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid a Borno
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid A Borno
  • Matasa 3 sun rasu yayin wanka a rafi a Bauchi
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Katsina, Sun Jikkata Mutane 2, Sun Sace Wasu
  • Zazzaɓin Lassa ya kashe mutum 151 a Nijeriya bana — NCDC
  • Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh