Amurka da China sun cimma sabuwar yarjejeniyar kasuwanci
Published: 11th, June 2025 GMT
Amurka da China sun cimma sabuwar yarjejeniyar kasuwanci da ke kawo karshen zaman tankiyar da aka soma tsakanin kasashen biyu tun bayan hawan Donald Trump karagar mulki.
Kasashen biyu sun cimma matsaya a kan kan cinikin wani rukini na ma’adinai da Chinar ke fitarwa, wadanda ake kira da sunan Terres Rares, wadanda ake yi amfani da shi wajen samar da lantarki da kuma makamashin da ake sabbintawa.
A baya a taron kasar Switzerland, Washington ta amince da rage haraji kan kayayyakin kasar China daga kashi 145 zuwa kashi 30 cikin 100, don musanya makamancin wannan mataki da Beijing ta dauka daga kashi 125% zuwa 10% kan kayayyakin Amurka, na tsawon kwanaki 90.
Shugaban Gwamnatin Jamus, Frederich Merz, ya yi marhabin da yarjejeniyar kasuwanci da aka cimma tsakanin Washington da Beijing a birnin Landan na Birtaniya.
Merz ya ce yana maraba da wannan yarjejeniya, kuma yana matukar Kungiyar Tarayyar Turai za ta yi nasara wajen rage rikice-rikicen kasuwanci da Amurka.
A watan Mayun da ya gabata ne China da Amurka suka cimma yarjejeniyar jinkirta aiwatar da sabon tsarin biyan harajin da suka lafta wa juna har sai bayan kwanaki 90, matakin da tun a lokacin aka yi tsammanin zai iya kawo karshen zaman tankiyar da ake yi tsakanin kasashen biyu mafi karfin tattalin arziki a duniya.
Sai dai a farkon makon nan ne China ta tabbatar da cewa wakilanta za su gana da takwarorinsu na Amurka a kasar Birtaniya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kasuwanci yarjejeniya
এছাড়াও পড়ুন:
Tattalin arzikin Nijeriya zai haɓaka cikin shekaru uku masu zuwa — Bankin Duniya
Bankin Duniya ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Nijeriya zai haɓaka ba tare da taɓarɓarewa nan da shekaru uku masu zuwa.
Bankin ya yi hasashen haɓakar ma’aunin tattalin arzikin cikin gida, GDP da kashi 3.6 cikin 100 a shekarar 2025, sai kashi 3.7 a shekarar 2026 da kuma kashi 3.8 a shekarar 2027.
Dalilin da babu abin da gwamnatin NNPP ta taɓuka a Kano — APC Amurka da China sun cimma sabuwar yarjejeniyar kasuwanciA cewar sabon rahoton tattalin arzikin duniya da Bankin ya fitar, ana sa ran za a tallafa wa matsakaicin lokaci na Nijeriya ta hanyar samar da ingantattun albarkatun mai, da gyare-gyaren da ake ci gaba da yi, da kuma farfado da ƙwarin gwiwar masu zuba jari.
Rahoton ya yi nuni da cewa, yayin da tattalin arzikin kasar ke shirin fadada, kalubale irin su hauhawar farashin kayayyaki, da matsalar canjin kudi, da kuma gibin kasafin kudi na ci gaba da zama babbar barazana ga ci gaba mai ɗorewa.
Bankin ya kuma kara da cewa, aiwatar da sauye-sauye a fannin tattalin arziki da gwamnatin Nijeriya ke yi, musamman ta fuskar farashin makamashi da tattara kuɗaɗen shiga, da sarrafa kuɗaɗen musaya, zai taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da waɗannan hasashen ci gaban.
Ana sa ran ci gaban Nijeriya a shekarar 2025 zai kasance matsakaici da kashi 3.3 cikin 100, yayin da matsalolin tsarin ke ci gaba da yin la’akari da saurin farfadowar tattalin arziki.
Bankin Duniya ya yi kira ga masu tsara manufofin Nijeriya da su ba da fifiko ga sauye-sauyen tsarin da ke inganta ci gaban kamfanoni masu zaman kansu, inganta ababen more rayuwa, da inganta jarin ɗan Adam don ɗorewar bunkasar tattalin arziki na dogon lokaci.