Aminiya:
2025-07-29@06:31:14 GMT

Amurka da China sun cimma sabuwar yarjejeniyar kasuwanci

Published: 11th, June 2025 GMT

Amurka da China sun cimma sabuwar yarjejeniyar kasuwanci da ke kawo karshen zaman tankiyar da aka soma tsakanin kasashen biyu tun bayan hawan Donald Trump karagar mulki.

Kasashen biyu sun cimma matsaya a kan kan cinikin wani rukini na ma’adinai da Chinar ke fitarwa, wadanda ake kira da sunan Terres Rares, wadanda ake yi amfani da shi wajen samar da lantarki da kuma makamashin da ake sabbintawa.

An kashe mutum 15 a sabbin hare-hare a Filato Mokwa: Zulum ya kai ziyarar jaje Neja, ya bayar da tallafin N300m

A baya a taron kasar Switzerland, Washington ta amince da rage haraji kan kayayyakin kasar China daga kashi 145 zuwa kashi 30 cikin 100, don musanya makamancin wannan mataki da Beijing ta dauka daga kashi 125% zuwa 10% kan kayayyakin Amurka, na tsawon kwanaki 90.

Shugaban Gwamnatin Jamus, Frederich Merz, ya yi marhabin da yarjejeniyar kasuwanci da aka cimma tsakanin Washington da Beijing a birnin Landan na Birtaniya.

Merz ya ce yana maraba da wannan yarjejeniya, kuma yana matukar Kungiyar Tarayyar Turai za ta yi nasara wajen rage rikice-rikicen kasuwanci da Amurka.

A watan Mayun da ya gabata ne China da Amurka suka cimma yarjejeniyar jinkirta aiwatar da sabon tsarin biyan harajin da suka lafta wa juna har sai bayan kwanaki 90, matakin da tun a lokacin aka yi tsammanin zai iya kawo karshen zaman tankiyar da ake yi tsakanin kasashen biyu mafi karfin tattalin arziki a duniya.

Sai dai a farkon makon nan ne China ta tabbatar da cewa wakilanta za su gana da takwarorinsu na Amurka a kasar Birtaniya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kasuwanci yarjejeniya

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan

Alkalin alkalan JMI Gholamhussain Muhsen Ejei, ya bayyana cewa, babu shakka gwamnatin kasar Amurka tana da hannu a hare-haren da ake dangantawa da kungiyar yan ta’adda ta Jaishul Zulm da ya faru a cikin wani kotu a garin Zahidan na lardin sistan Baluchistan a cikin yan kwanakin da suka gabata.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto alkalin alkalan yana fadar haka a lokacinda ya kai ziyara a gaisuwar wadanda abin ya shafa. Ya kuma bukaci mataimakinsa ya gabatar da dukkan bukatun da wadanda abin ya shafa suka gabatar.

A cikin maganar sa alkalin alkalan ya bayyana cewa, an halaka mutane uku a musayar wuta da yan ta’addan a kusa da kotun. Sannan JMI ta samar da shahidai 6 sannan wasu 22 suka ji rauni.

Yankin Sistan Baluchistan dai ya dade yana fama da hare-hare na wannan kungiyar, kuma tana da sansani a cikin kasar Pakistan wacce take makobtaka da kasar a kudu maso gabacin kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan
  • Amurka Ta Dakatar Da Bai Wa ‘Yan Kasar Nijar Bisa Shiga Cikin Kasarta
  • Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan
  • Iran Da Afganistan Sun Tattauna Dangane Da Komawar Afganawa Gida
  • VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
  • Kasar Iran Ta Ce Tana Hulda Da Amurka Ta Hanyar Masu Shiga Tsakani
  • Shugaban Kasar Amurka Ya Shiga Cikin Sahun Masu Mafarkin Rusa Kungiyar Hamas
  • Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya
  • Yawan Mutanen Da Suka Rayukansu A Rikicin Lardin Suwaida Na Kasar Siriya Ya Kai 1,400