Aminiya:
2025-11-03@09:32:51 GMT

Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara

Published: 13th, June 2025 GMT

Dakarun sojin Nijeriya sun yi nasarar kashe wasu ’yan ta’adda yayin wani samame da suka kai garin Kunchin Kalgo a ƙaramar hukumar Tsafe da ke Jihar Zamfara.

A sanarwar da rundunar ta wallafa a shafinta na X ranar Alhamis, ta ce a ranar 10 ga watan Yuni ne rundunar FANSAN YAMMA ta kashe ƙasurguman ‘yan ta’addan da suka haɗa da Auta da Abdul Jamilu da kuma Salisu.

Leroy Sane ya koma Galatasaray Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu

“Waɗannan ’yan ta’adda suna da alaƙa da ayyukan tashin hankali da ta’addanci da ake yawan samu a yankin gaba ɗaya.

“Wannan farmakin dai na nuni da wani gagarumin koma baya ga masu aikata laifuka, wanda ke dagula zaman lafiya da tsaro a yankin,” in ji sanarwar.

Bayanan sirri na farko-farko sun nuna cewa an kashe ƙarin wasu shugabannin ’yan ta’adda, ciki har da wani da aka fi sani da Babaye a lokacin harin.

Kazalika, a wani lamarin daban, rahotanni sun ce an kashe Sale Ado Madele da aka fi sani da Sarki, babban ɗan shugaban ‘yan bindiga Ado Alieru.

A wani lamarin mai kama da haka, sojojin sun kuma kashe wasu ’yan ta’adda goma da suka taru a kusa da wata tashar mai da ke garin Danjibga.

Ana kyautata zaton ‘yan ta’addan na cikin wani gungun hadin-gwiwa da Dogo Sule ya haɗa domin kai hari.

Rundunar sojojin Nijeriya ta ce tana ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da kuma maido da dauwamammen zaman lafiya a fadin Jihar Zamfara da yankin Arewa maso Yamma.

“Wannan aiki yana ƙara jaddada ƙudurinmu na wargaza hanyoyin sadarwar ‘yan ta’adda tare da gurfanar da masu aikata laifuka a gaban ƙuliya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan ta adda Jihar Zamfara yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar amfani da ƙarfin soji kan Najeriya matuƙar gwamnatin ƙasar ba ta dakatar da kisan da ’yan ta’adda masu iƙirarin jihadi ke yi wa Kiristoci ba.

A yammacin jiya Asabar ne Trump ya umarci Ma’aikatar Yaƙin Amurka ta Pentagon da ta soma tsara yadda za a kai hari Nijeriya bayan da ya yi zargin cewa ana yi wa Kiristoci kisan gilla a ƙasar.

Cikin wani saƙo da ya wallafa  a shafinsa na Truth Social, Trump ya ce Amurka a shirye ta ke ta aike da sojoji da manyan makamai cikin Najeriya don bai wa Kiristocin kariya.

Barazanar shugaban na Amurka na zuwa ne kwana guda bayan ya yi iƙirarin cewa an kashe Kiristoci aƙalla 3,100 a Nijeriya ba tare da ya bayyana takamaimai inda ya samu waɗannan alƙaluma ba.

“Muddin gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bari ana kashe Kiristoci, Amurka za ta dakatar da dukkan tallafin da take bai wa Nijeriya nan-take, kuma mai yiwuwa za ta shiga wannan ƙasƙantacciyar ƙasar, cike da ƙarfin gwiwa domin kawar da ’yan ta’adda masu kaifin kishin Musulunci waɗanda ke yin wannan ta’asa,” in ji Trump.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa