LEADERSHIP ta tuna cewa, gwamnatin jihar da jami’an tsaro sun fuskanci matsin lamba daga mazauna yankunan da lamarin ya shafa domin shawo kan lamarin.

 

Fanwo, ya ba da tabbacin cewa, gwamnati ta yi shiru, amma tana samun nasara a yakin da take da masu aikata laifuka ta karkashin kasa, musamman masu garkuwa da mutane a jihar.

 

Ya ce, nasarar da gwamnati ta samu ya biyo bayan ingantattun tsare-tsare da zurfafa hadin gwiwar hukumomin tsaro da nufin tabbatar da tsaro da walwalar kowane dan jihar Kogi.

 

Yayin da take jajantawa iyalan wadanda hare-haren na baya-bayan nan ya shafa, gwamnatin jihar ta jaddada cewa, bai kamata a yi amfani da irin wadannan kalubalen wajen yada labaran karya ko firgita jama’a ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

 Gaza: Ana Ci Gaba Da Samun Shahidai Da Yunwa Take Kashewa A Gaza

A daidai lokacin da aka cika kwanaki 659 daga fara kisan kiyashin Gaza, sojojin Sahayoniya suna ci gaba da killace yankin da hana shigar da abinci da magani.

Ma’aiktar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa ya zuwa wannan lokacin jumillar wadanda yunwa ta kashe sun kai 122 daga cikinsu da akwai kananan yara 83.

Da jijjifin safiyar yau Asabar, majiyar asibitin “Nasr’ ta sanar da cewa wata jaririya ta yi shahada saboda rashin abinci mai gina jiki. Haka nan kuma ta ce, jaririyar ‘yar watanni 6 da haihuwa ta yi shahada ne saboda rashin abinci mai gina jiki da kuma magani saboda takunkumin da HKI ta kakabawa yankin na Gaza.

Babban jami’iin gudanarwa na ma’aikatar kiwon lafiya a Gaza Dr. Munir al-Bursh ya sanar da cewa; Ana kara samun masu mutuwa saboda yunwa, musamman ma dai a tsakanin kananan yara.

Al-Bursh ya fada wa tashar talabijin din al-jazira cewa; Yunwa saboda rashin abinci da kuma rashin Magani ya sa jariran da suke cikin  mata 3,000 sun mutu.

Haka nan kuma ya nuna mamakinsa akan yadda duniya ta gajiya wajen iya shigar da madarar jarirai cikin yankin Gaza domin ceto da rayuwar kananan yara da jarirai.

A wannan tsakanin ne dai Asusun kananan yara na MDD ( Unicef) ya yi gargadi akan mummunan halin da yaran Gaza suke ci gaba da shiga saboda rashin abinci mai gina jiki.

Ita kuwa shugabar hukumar Agaji ta kasa da kasa “Rd Cross” ta yi kira ne da a kawo karshen wahalhalu da bala’in da aka jefa mutane a Gaza, cikin gaggawa ba tare da ba ta lokaci ba.

A wani labarin na daban, kafafen watsa labarun HKI sun ce, sojojin Sahayoniya sun lalata tarin abinci mai yawa da aka ware domin shigar da shi zuwa yankin Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Dashen Itatuwa Na Bana
  • Tsofaffin Gwamnoni Sun Ziyarci Tinubu Tare Da Bashi Shawarwari Kan Matsalolin Tsaro
  •  Gaza: Ana Ci Gaba Da Samun Shahidai Da Yunwa Take Kashewa A Gaza
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Naira Biliyan 3.5 Wajen Gina Shaguna A Farm Centre
  • Jihar Jigawa Na Kara Bullo Da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Bukata Ta Musamman
  • Matsalar Tsaro: Sarakuna Sun Bukaci Gwamnati Ta Canza Salo
  • Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Karyata Rade-radin Sayarda Makarantar Yusuf Dan-tsoho 
  • Gwamnatin Yobe ta bada tallafi ga iyalan ’yan banga da suka rasu
  • Gwamnatin Bauchi Ta Cire Shugaban Makaranta Kan Satar Kayan Gwamnati
  • Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja