Sojoji sun kashe wani kwamandan ’yan ta’adda a Yobe
Published: 9th, June 2025 GMT
Rundunar Sojojin Nijeriya ta ce ta kashe ’yan ta’adda da dama a cikin wasu jerin hare-hare na sama da na ƙasa da suka kai sansanonin ’yan ta’addan Boko Haram da ISWAP da ke Nzalgana, a ƙaramar hukumar Gujba ta Jihar Yobe a Arewa maso Gabashin Nijeriya.
Sanarwar da rundunar ta wallafa a shafukanta na sada zumunta ta ce hare-haren da sojojin suka ƙaddamar da sanyin safiyar Litinin 9 ga watan Yuni sun yi sanadin mutuwar wani babban kwamandan Boko Haram a ƙauyukan Ngorgore da Malumti, Ameer Malam Jidda.
Duk da cewa sanarwar ba ta yi ƙarin bayani game da jerin hare-haren ba, sai dai Zagazaola Makama, wani kwararren kan lamuran tsaron a yankin, ya ruwaito cewa sojojin sun ƙwato bindigogi ƙirar AK47 da harsasai da kuma babur daga hannun kwamandan da aka kashe.
Sai dai kuma sanarwar ta sojojin ta bayyana cewa sojojin sun sake samun ƙarin makamai da gawarwakin ‘yan ta’adda a Abadam bayan arangamar da suka yi da ‘yan ta’addan kwanan nan a Mallam Fatori.
Cikin ‘yan makonnin nan dai an yi ta samun rahotannin hare-haren da ‘yan ta’adda ke kai wa sansanonin sojoji a yankin.
Kazalika sojojin ƙasar su ma suna kai hare-hare ta sama kan sansanonin ‘yan ta’addan a yankin domin su hana su iya kai irin hare-haren da suke kai wa kan sojoji.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram Jihar Yobe yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
Wani mutum ya rasu a gidan karuwai bayan ziyartar ’yan mata
Wani mutum da ba a gano sunansa ba ya mutu bayan da ya shiga wani gidan karuwai domin ganawa da ’yan mata masu zaman kansu a birnin Fatakwal.
Lamarin ya faru ne a ranar Lahadi, inda rahotanni suka ce mamacin ya shiga gidan karuwai ne domin yin hulɗa da ’yan mata, sai dai ba a tabbatar da abin da ya jawo mutuwarsa ba.
Jami’ar Hulɗa da Jama’a ta Rundunar ’Yan Sandan Jihar Ribas, SP Grace Iringe-Koko, ta tabbatar da faruwar lamarin a ranar Litinin, inda ta ce an miƙa batun zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Jihar (SCID) domin gudanar da cikakken bincike.
Wasu majiyoyi daga cikin gidan karuwan sun bayyana cewa wani ma’aikacin otal ɗin da ke kula da wurin ya yi faɗa da mamacin kafin daga bisani ya yanke jiki ya faɗi ya mutu.
Matar tsohon Shugaban Ƙasa Shagari ta rasu EFCC na neman tsohon Gwamnan Bayelsa ruwa a jalloMajiyar ta ƙara da cewa an garzaya da mutumin asibiti domin ba shi agajin gaggawa, amma daga bisani likitoci suka tabbatar da mutuwarsa.
Rahotanni sun ce an kama wani mutum daga cikin gidan matan da ake zargi da hannu a lamarin, kuma rundunar ’yan sanda ta jihar ta ta fara bincike a kai.
SP Grace Iringe-Koko ta kuma tabbatar da cewa an kama mutum ɗaya da ake zargi, kuma sashen ’yan sanda na Azikiwe ya miƙa shari’ar zuwa SCID domin gudanar da bincike mai zurfi.
Sai dai bayan faruwar lamarin, an lura dukkan ’yan mata masu zaman kansu da ke yawo a cikin da wajen gidan karuwan sun yi layar zana.