“Gwamnatin ta yi hakan ne, sakamakon tabbatar da ganin an fara aiki a kamfanin daga nan zuwa karshen watan Mayun shekarar 2025.

“Gwamnatin Jihar da shude ce ta bai wa kamfanin kwangilar da kuma wani kamfani da ke Kasar Indiya aikin, inda gwamnatin ta zuba dala biliyan 12 a kamfanin,” in ji Hamza.

Sai dai, ya bayyana cewa; saboda kasancewar wasu dalilai, ba a samu cimma wata gagarumar nasarar a zo a gani ba a kan aikin.

Ya sanar da cewa, a watan da ya gabata ne, gwamnatin jihar ta sake yin nazari kan yarjeniyar ta baya da aka kulla, wadda kuma za a dawo, domin a ci gaba da yin aikin.

Babban Sakaren ya kara da cewa, manyan batutuwan da suka zama hummulhaba’isin dakatar da aikin su ne, kaluabalen rashin tsaro, amma yanzu, an sake yin nazari a kan sake dawo da ci gaba da aikin.

“An samar da daukacin Injinonin kamfanin, domin gudanar da aikin, amma kalubalen rashin tsaro ya jawo koma baya,” a cewar Babban Sakataren.

Ya yi nuni da cewa, idan aka fara gudanar da aikin, zai kara sanya wa manoman jihar samun wadataccen takin zamani, a kuma kan farashi mai rashusa.

Ita ma da take yi wa ‘yan jaridar karin bayani tun da farko, kwamishinan samar da bayanai da tsare-tsare, Binta Mamman ta bayyana cewa; an kara samar da tsaro a yankin, wanda hakan zai bai wa manoman jihar, damar komawa gonakinsu, domin fara aikin noma na bana.

“A shekarun baya, manoman jihar da dama, ba sa iya zuwa gonakinsu, domin yin noma, amma yanzu ba su da wata matsala ko fargaba wajen zuwa gonakin nasu, domin yin noma,” a cewar Binta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sallah: ’Yan sanda sun yi alƙawarin tabbatar da tsaro a Gombe

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta shirya tsare-tsaren tsaro domin ganin an yi Sallar Idi cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya.

Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana cewa za a tura ’yan sanda da sauran jami’an tsaro zuwa filayen Idi, Masallatai, da wuraren taro domin kula da tsaro da zirga-zirgar jama’a.

Ambaliyar Mokwa: An gano gawar yara 7, jama’a na neman agaji Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a Kano

Za a sanya ido sosai a manyan hanyoyi musamman waɗanda ke kai wa zuwa wuraren sallah, domin rage cunkoso da sauƙaƙa zirga-zirgar jama’a.

An ware ƙofofin shiga da fita a filayen Sallah domin a riƙa duba mutane da kayan da suke ɗauke da su.

Rundunar ta kuma roƙi jama’a da su bi waɗannan ƙa’idoji domin kauce wa jinkiri.

’Yan sandan sun gargaɗi mutane da ka da su ajiye motoci ba bisa ƙa’ida ba, sannan su kaucewa yin salla a tsakiyar hanya, ko toshe hanyoyin fita.

Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, ya roƙi mutane da su bayar da haɗin kai wajen bin doka, tare da kasancewa masu lura da duk wani abu da zai kawo barazana.

Ya kuma gargaɗi masu laifi da su guji duk wani abu da zai jawo tashin hankali a jihar.

Hakazalika, ya taya al’ummar Gombe murnar Sallar Idi, tare da tabbatar musu cewa ’yan sanda za su ci gaba da kare lafiyar jama’a domin a yi bukukuwan sallah cikin kwanciyar hankali.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
  • Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
  • 2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
  • An Kashe Sojojin HKI Da Dama Sannan Wasu Sun Ji Raune A Garin Khan Yunus A Jiya Jumma
  • Gwamnan Akwa Ibom ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC
  • Farfesa Jibril Amin Tsoho Ministan Ilim Da, Manfetur A Najeriya Rasu Yana Dan Shekara 85 A Duniya
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus
  • Mahajjata Aikin Hajjin Bana Sun Tafi Tsayiwar Arafat A Yau Alhamis Don Fara Ginshikin Aikin Hajj
  • Sallah: ’Yan sanda sun yi alƙawarin tabbatar da tsaro a Gombe