Matawalle: Kofarmu Abude Take Idan Gwamna Dauda Lawal Na San Shigowa Jamiyyar APC
Published: 9th, June 2025 GMT
Tsohon gwamanan Jihar Zamfara kuma Karamin Ministan Tsaro, Bello Muhammed Matawalle ya bayyana cewa, kofar Jam’iyyar APC abude take idan gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal na Jamiyyar PDP na bukatar shigowa Jamiyyar.
Ministan ya bayyana haka ne a Mahaifarsa Maradun a lokacin ziyar Sallah da magoya bayan Jam’iyyar APC na Kananan Hukumomi 14 suka kai masa a gidansa da ke Maradun cikin Jihar Zamfara.
Matawalle ya bayyana cewa, muna jin rade-radin cewa , gwamna Dauda zai dawo Jam’iyyar APC sakamakon Jam’iyyar su ta PDP na fama da matsalar rikice-rikice. Domin yanzu haka da Sallar nan daya daga cikin gwamnonin PDP ya dawo APC A Legas.
Don haka, Kofarmu a bude take ga gwamna Dauda Lawal, zuwansa APC dan bamu kyama, kowa da kowa namune Indai ya shigo wannnan Jam’iyyar mai albarka ta APC.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa
PPRO ta bayyana cewa binciken farko ya nuna cewa wanda ake zargin yana auren mahaifiyar wanda aka cutar (da sakaya sunanta).
“An bayyana cewa ya yi lalata da yarinyar a lokacin da mahaifiyarta ke barci, yana shiga dakinta kuma yana aikata abubuwan da ba su dace ba a lokuta da dama.
“Wakil ya ce, “Yarinyar na shan wahala amma duk da haka ta kame bakinta sai da lamarin ya ta’azzara sannan ta fada wa makwabta, wanda hakan ya kai ga daukar matakin kama wanda ake zargi da aikata laifin,”
Ya ce a lokacin da ake yi masa tambayoyi an ruwaito wanda ake zargin ya amsa laifinsa.
“An kwashe wanda abin ya rutsa da shi zuwa asibiti domin duba lafiyarsa da kulawa.
“Kwamishanan ‘yansandan Jihar Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu ya bayar da umarnin mika karar zuwa sashen binciken manyan laifuka na jihar domin gudanar da bincike mai zurfi, daga nan kuma za a gurfanar da wanda ake zargin zuwa kotu.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp