Ma’aikatar kiwon lafiya na kasar Iran ta bayyana cewa kasar a halin ayanzu tana daga cikin kasashe uku na gaba a kan abinda ya shafi samun isasshen abinci mai lafiya da kuma wadatacce a cikin kasar.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan kiwon lafiya Muhammad Reza Zafarkandi yana fadar haka a jiya litinin a taron raya ranar abinci da duniya wanda aka gudanar a dakin taro na hukumar gidajen radio da talabijin a nan birnin Tehran.

Ministan ya kara da cewa, samun abinci mai gina jiki da kuma bada sinadaran da jiki yake bukata yana daga cikin abubuwan da suke bada lafiya ga jiki.

Har’ila yau wannan yana kwantar da hankalin mutanen ko wace kasa wacce take da wannan matsayin na samar da abinci da kuma lamunin lafiyar abincin.

Ministan ya ce akwai kamfanonin samar da abinci a cikin kasar kimani 17,000 wadanda ma’aikatar take kula da dukkan abincin da suke samarwa, don tabbatar da lafiyansu da kuma ingancinsu kafin su sayarwa mutane.

Sannan ma’aikatar tana da dakunan bincike har 450 wadanda suke gwada lafiyar abincin da wadannan kamfanoni suke samarwa a duk fadin kasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda masu yi wa kasa hidima za su ci arzikin yankunan da suke aiki

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Bayan hadin kai da karfafa fahimtar juna wadanda hidimar kasa take kawowa, akan samu wasu masu hidimar da sukan yi amfani da duk wata dama da suka samu don neman na sakawa a bakin salati.

Yayin da wasu masu hidimar kasa sukan kama sana’a ko su saka hannun jari a inda aka tura su, wasu kuwa komawa garuruwansu suke yi bayan sun kammala.

NAJERIYA A YAU: Cututtukan da rumar daki ke haifarwa ga jikin mutum DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta

Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan irin damar da masu yi wa kasa hidima suke da ita a garuruwan da aka tura su.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Da Eu Sun Fara Tattaunawa A Istambul
  • Mutanen A Netherlands Suna Zaman Dirshen Saboda Gaza
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Ce: Taro Tsakanin Iran Da Tawagar Kasashen Turai Dama Ce Ta Gyarar Tunanin Tarai
  • Hukumar Ba Da Agajin Jin Kai Ta ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinawa Ta “UNRWA” Ta Sanar Da Kashe Ma’aikatan 330 A Gaza
  • NAJERIYA A YAU: Yadda masu yi wa kasa hidima za su ci arzikin yankunan da suke aiki
  • Iran: Iran Tana Cikin Kasashe Biyar Na Duniya Da Suka Ci Gaba Wajen Kiwon Dabbobi
  • Fiye Da  Falasdinawa 111 Ne Su Ka Yi Shahada Saboda Yunwa A Gaza
  • Matar aure ta kashe mijinta a kan abinci a Yobe
  •  Fiye Da  Kungiyoyin 100 A Duniya Sun Yi Gargadi Akan Halin Yunwa Da HKi Ta Jefa Mutanen Gaza A Ciki
  • WFP zai dakatar da tallafin abinci da kiwon lafiya a Nijeriya