Iran Tana Daga Cikin Kasashe 3 A Nahiyar Asiya Wadanda Suke Da Lamunin Samun Isasshen Abinci
Published: 10th, June 2025 GMT
Ma’aikatar kiwon lafiya na kasar Iran ta bayyana cewa kasar a halin ayanzu tana daga cikin kasashe uku na gaba a kan abinda ya shafi samun isasshen abinci mai lafiya da kuma wadatacce a cikin kasar.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan kiwon lafiya Muhammad Reza Zafarkandi yana fadar haka a jiya litinin a taron raya ranar abinci da duniya wanda aka gudanar a dakin taro na hukumar gidajen radio da talabijin a nan birnin Tehran.
Ministan ya kara da cewa, samun abinci mai gina jiki da kuma bada sinadaran da jiki yake bukata yana daga cikin abubuwan da suke bada lafiya ga jiki.
Har’ila yau wannan yana kwantar da hankalin mutanen ko wace kasa wacce take da wannan matsayin na samar da abinci da kuma lamunin lafiyar abincin.
Ministan ya ce akwai kamfanonin samar da abinci a cikin kasar kimani 17,000 wadanda ma’aikatar take kula da dukkan abincin da suke samarwa, don tabbatar da lafiyansu da kuma ingancinsu kafin su sayarwa mutane.
Sannan ma’aikatar tana da dakunan bincike har 450 wadanda suke gwada lafiyar abincin da wadannan kamfanoni suke samarwa a duk fadin kasar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jirgin Ruwa “Madeleine” Dake Son Karya Takunkumin Gaza Yana Ci Gaba Da Tafiya
Jirgin ruwan na “Madeleine” shi ne na 36 a cikin jerin jiragen ruwan ‘yanci da suke son karya takunkumin da aka kakabawa yankin Gaza tun 2007.
A cikin wannan jirgin ruwan da akwai ‘yan gwgawarmaya masu rajin kare hakkin bil’adama su 12 da su ka fito daga kasashe daban-daban, yana kuma dauke da kayan agaji na abinci da magani.
Jirgin ruwan ya samo sunansa ne daga wata Bafalasdiniya mai suna; Madeleine Kulaib, wacce ita ce macen farko ta Falasdinu da ta kware a sana’ar kama kifi bayan da mahaifinta ya yi shahada a yayin yakin da HKI ta shelanta akan Gaza a 2023.
Jirgin ruwan na “Madline” ya taso ne daga kasar Italiya, wata daya bayan da jirgin sama maras matuki na HKI ya kai hari akan wani jirin ruwan wanda ya nufi Gaza akan gabar ruwan Malta.
Daga cikin kayan da jirgin ruwan yake dauke da shi a kawai madarar jarirai, shinkafa, da kuma magunguna da injinan tace ruwa. Haka nan kuma yana dauke da gabobin jikin dan’adam na roba na yara, saboda a yi wa yaran Gaza da Isra’ila ta mayar masakai dashe.
Mafi yawancin masu fafutukar dake cikin jirgin sun fito ne daga kasashen turai, kamar Sweeden Jamus da Faransa. Sai kuma wasu daga Holland da Brazil.