HausaTv:
2025-06-12@05:49:06 GMT

Isra’ila ta sake kashe Falasdinawa a wurin rabon tallafi

Published: 10th, June 2025 GMT

Bayanai daga Falasdinu na cewa akalla mutum 20 ne sukayi shahada a wani sabon harin da sojojin Isra’ila suka kai a lokacin da ake rabon abinci a Gaza.

Shaidun gani da ido sun ce sojojin Isra’ila sun bude wuta da safiyar Talatar nan, kan Falasdinawa da za su karbi kayayyaki a tsakiyar Gaza a wani wuri da ke karkashin gidauniyar agaji ta Gaza (GHF).

Jami’an Falasdinawa sun kara da cewa sama da mutane 120 ne suka jikkata a harin na Isra’ila.

Harin na baya-bayan nan ya zo ne sa’o’i bayan da sojojin Isra’ila suka kashe Falasdinawa 14 da suka taru a wajen wata cibiyar GHF da ke kudancin Rafah.

Kisan na yau ya sanya adadin wadanda sukayi shahada a wajen rabon abinci a Gaza sanadin hare-haren Isra’ila zuwa 110 tun ranar 27 ga watan Mayu, a tsarin rabon abincin na GHF da ke samun goyon bayan Isra’ila da Amurka.

Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa ne ke sukan tsarin rabon tallafin wanda wasu ke dangantawa da tarkon mutuwa.

Halin da ake ciki na jin kai a Gaza ya kai intaha inda kungiyoyi musamman MDD ke bayyana shi da mafi muni a duniya.

Tun bayan fara yakin kisan kare dangi da Isra’ila ta kaddamar a ranar 7 ga Oktoba, 2023, adadin Falasdinawa da sukayi shahada ya kai 54,927, yawancinsu mata da kananan yara, sannan wasu kusan 126,615 sun jikkata.

A watan Nuwamba 2024, Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ta ba da sammacin kama Firayim Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da tsohon ministansa na soja Yoav Gallant, bisa zarginsu da laifukan yaki da cin zarafin bil’adama a Gaza.

Haka zalika kuma ana zargin gwamnatin Isra’ila da kisan kare dangi a gaban kotun kasa da kasa ta ICJ saboda ta’addancin da ta aikata a zirin Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Wasu Jiragen Ruwa Na  Ceto Da Jin Kai  Sun  Tashi Daga Tunisiya Zuwa Gabar Ruwan Gaza

Jiragen ruwan wadanda aka bai  wa sunan: “Jajurcewa” za su tashi ne daga Tunisiya jim kadan bayan da sojojin HKI su ka hana wani jirgin ruwan dake dauke da masu fafutuka daga kasashen turai,isa gabar ruwan Gaza.

Jirgin ruwan na ” Jajurcewa’ zai bi ta ruwan Libiya, sannan Masar daga can kuma ya nufi gabar ruwan Gaza.

Jiragen ruwan dai suna dauke da masu fafutuka 7,000 daga kasashen Tunisiya, Moroko, Aljariya, Murtaniya, da Libiya.

Kwamitin kasa da kasa domin karya killace Gaza, wanda ya shirya wannan tafiyar, ya kuma yi wani kiran ga ‘yan fafutuka a duniya da su shirya wasu tafiye-tafiyen ta ruwa zuwa Gaza, domin kawo karshen killace yankin da aka yi tun 2007.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gini ya kashe Ba’indiye a Zariya
  • Jagora Ya Bambance Tsakanin Majalisun Dokokin Kasashe A Fagen Gudanar Da Ayyukan Kasa
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutane 8 A Jihar Filato
  • Falasdinawa Masu Yawa Sun Yi Shahada A Cibiyoyin Raba Kayan Agaji
  • Al’ummomi Daga Sassan Duniya Suna Yin Tofin Allah Tsine Kan Sace Masu Fafatuka A Kan Hanyarsu Ta Zuwa Gaza 
  • Bom ya kashe masu yawon murnar sallah a Sakkwato
  • Isra’ila ta ƙwace jirgin ruwa a hanyar kai agaji Gaza
  • Wasu Jiragen Ruwa Na  Ceto Da Jin Kai  Sun  Tashi Daga Tunisiya Zuwa Gabar Ruwan Gaza
  • Ministan Leken Asiri Na Iran Ya Yi Karin Bayani Kan Nasarar Samun Bayan Tsaron HKI