Isra’ila ta sake kashe Falasdinawa a wurin rabon tallafi
Published: 10th, June 2025 GMT
Bayanai daga Falasdinu na cewa akalla mutum 20 ne sukayi shahada a wani sabon harin da sojojin Isra’ila suka kai a lokacin da ake rabon abinci a Gaza.
Shaidun gani da ido sun ce sojojin Isra’ila sun bude wuta da safiyar Talatar nan, kan Falasdinawa da za su karbi kayayyaki a tsakiyar Gaza a wani wuri da ke karkashin gidauniyar agaji ta Gaza (GHF).
Jami’an Falasdinawa sun kara da cewa sama da mutane 120 ne suka jikkata a harin na Isra’ila.
Harin na baya-bayan nan ya zo ne sa’o’i bayan da sojojin Isra’ila suka kashe Falasdinawa 14 da suka taru a wajen wata cibiyar GHF da ke kudancin Rafah.
Kisan na yau ya sanya adadin wadanda sukayi shahada a wajen rabon abinci a Gaza sanadin hare-haren Isra’ila zuwa 110 tun ranar 27 ga watan Mayu, a tsarin rabon abincin na GHF da ke samun goyon bayan Isra’ila da Amurka.
Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa ne ke sukan tsarin rabon tallafin wanda wasu ke dangantawa da tarkon mutuwa.
Halin da ake ciki na jin kai a Gaza ya kai intaha inda kungiyoyi musamman MDD ke bayyana shi da mafi muni a duniya.
Tun bayan fara yakin kisan kare dangi da Isra’ila ta kaddamar a ranar 7 ga Oktoba, 2023, adadin Falasdinawa da sukayi shahada ya kai 54,927, yawancinsu mata da kananan yara, sannan wasu kusan 126,615 sun jikkata.
A watan Nuwamba 2024, Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ta ba da sammacin kama Firayim Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da tsohon ministansa na soja Yoav Gallant, bisa zarginsu da laifukan yaki da cin zarafin bil’adama a Gaza.
Haka zalika kuma ana zargin gwamnatin Isra’ila da kisan kare dangi a gaban kotun kasa da kasa ta ICJ saboda ta’addancin da ta aikata a zirin Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas Ta Karyata Gwamnatin Mamayar Isra’ila Kan Shirga Karya Don Kare Muggan Manufofinta
Kungyar Hamas ta bayyana cewa: Gmanatin mamayar Isra’ila ta ƙirƙiri ƙarya don kare kisan gillar da ta yi a Gaza
Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta tabbatar da cewa: Zargin da kakakin rundunar sojin mamayar Isra’ila ya gabatar dangane da yin amfani da hasumiyai a birnin Gaza domin aikin soji ba komai ba ne illa karairayi na zahiri da suke nufin kare laifukan da ake aikatawa da kuma boye barnar da ake yi a birnin Gaza, kamar yadda a baya sojojin mamaya suka lalata garuruwan Rafah, Khan Younis, Jabaliya, Beit Hanoun, da Beit Lahiya.
A cikin wata sanarwa da kungiyar Hamas ta fitar ta bayyana cewa, zargin mamaya na cewa kungiyar Hamas na amfani da fararen hula a matsayin garkuwar dan adam tare da hana su ficewa daga Gaza, yaudara ce karara da ke nuna rashin mutunta ra’ayin al’ummar kasa da kasa tare da tabbatar da dagewar da take yi na ci gaba da kisan kiyashi kan fararen hula da ba su ji ba ba su gani ba da kuma raba su da muhallinsu da karfi da nufin korar su daga zirin Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha September 17, 2025 Chadi: Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa September 17, 2025 Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila September 17, 2025 Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza September 17, 2025 Iran da Saudiyya sun bukaci hadin kan Musulmi game da halin da ake a yankin September 17, 2025 Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci