Isra’ila ta sake kashe Falasdinawa a wurin rabon tallafi
Published: 10th, June 2025 GMT
Bayanai daga Falasdinu na cewa akalla mutum 20 ne sukayi shahada a wani sabon harin da sojojin Isra’ila suka kai a lokacin da ake rabon abinci a Gaza.
Shaidun gani da ido sun ce sojojin Isra’ila sun bude wuta da safiyar Talatar nan, kan Falasdinawa da za su karbi kayayyaki a tsakiyar Gaza a wani wuri da ke karkashin gidauniyar agaji ta Gaza (GHF).
Jami’an Falasdinawa sun kara da cewa sama da mutane 120 ne suka jikkata a harin na Isra’ila.
Harin na baya-bayan nan ya zo ne sa’o’i bayan da sojojin Isra’ila suka kashe Falasdinawa 14 da suka taru a wajen wata cibiyar GHF da ke kudancin Rafah.
Kisan na yau ya sanya adadin wadanda sukayi shahada a wajen rabon abinci a Gaza sanadin hare-haren Isra’ila zuwa 110 tun ranar 27 ga watan Mayu, a tsarin rabon abincin na GHF da ke samun goyon bayan Isra’ila da Amurka.
Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa ne ke sukan tsarin rabon tallafin wanda wasu ke dangantawa da tarkon mutuwa.
Halin da ake ciki na jin kai a Gaza ya kai intaha inda kungiyoyi musamman MDD ke bayyana shi da mafi muni a duniya.
Tun bayan fara yakin kisan kare dangi da Isra’ila ta kaddamar a ranar 7 ga Oktoba, 2023, adadin Falasdinawa da sukayi shahada ya kai 54,927, yawancinsu mata da kananan yara, sannan wasu kusan 126,615 sun jikkata.
A watan Nuwamba 2024, Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ta ba da sammacin kama Firayim Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da tsohon ministansa na soja Yoav Gallant, bisa zarginsu da laifukan yaki da cin zarafin bil’adama a Gaza.
Haka zalika kuma ana zargin gwamnatin Isra’ila da kisan kare dangi a gaban kotun kasa da kasa ta ICJ saboda ta’addancin da ta aikata a zirin Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Za mu ba da damar shigar da kayan agaji a Gaza — Isra’ila
Isra’ila ta ce za ta bai wa ayarin Majalisar Dinkin Duniya damar shiga Gaza domin raba kayan agaji da magani, bayan makonni na matsin lamba daga hukumomi da kasashen duniya.
Sanarwar da rundunar sojin Isra’ila ta fitar ranar Asabar, ta ce ta bayar damar komawa jefa kayan agajin ta jiragen sama – abin da aka ce bai wadatar ba, baya ga hadarin da ke tattare da shi.
Super Falcons ta lashe gasar WAFCON karo na 10 bayan doke Maroko ADC ce kaɗai za ta iya magance matsalolin Arewa — David MarkRundunar sojin ta ce ta fara aiwatar da wasu jerin matakai na inganta kai agajin a yankunan da ke da tarin jama’a
Hakan dai na zuwa ne a yayin da Isra’ilar ke sci gaba da fuskantar matsin lamba daga hukumomi da kasashen duniya da ke bayyana damuwa kan al’ummar Falasdinawa a Zirin Gaza za su fada cikin mummunan bala’in yunwa.
A bayan nan dai Isra’ila ta takaita shigar da kayan agajin da magunguna tsawon watanni ga al’ummar yankin su miliyan biyu, a yayin da take ci gaba da musanta abin da ta kira ikirarin haddasa yunwa ga al’ummar ta Gaza da gangan.
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito kafofin Falasdinawa suna tabbatar da ci gaba da aikin jefa kayan agajin ta sama, a yankin arewacin Gaza.
Tun daga farkon watan Maris ne Isra’ila ta dakatar da bayar da dukkanin kayan agajin, amma ta bayar da damar bayarwa amma da sababbin sharuda a watan Mayu.
Isra’ila na ci gaba da luguden wuta a GazaAƙalla mutane 25 ne suka mutu a wasu hare-hare ta sama da kuma ta ƙasa da sojojin Isra’ila suka kai cikin dare a yankin Gaza.
Jami’an kiwon lafiya a asibitin Shifa da aka kai gawarwakin mutanen, sun ce mafi yawancinsu an kashe sune ta hanyar harbi da bindiga, a lokacin da suke dakon isowar motocin kayan agaji ta mashigar Zikim.
Wannan dai na zuwa ne dai-dai lokacin da tattaunawar da ake yi don cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da Hamas ta fuskanci koma baya, sakamakon yadda Amurka da Isra’ila suka janye wakilansu a ranar Alhamis.
A ranar Juma’a ce firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, ya ce gwamnatinsa na duba yuwuwar cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakaninsu da Hamas, kalaman da ke zuwa dai-dai lokacin da jami’in Hamas ke cewa ana saran a mako mai zuwa ne za su ci gaba da tattaunawa kan batun.
Ƙasashen Masar da Qatar waɗanda ke shiga tsakani a tattaunawar tare da Amurka, sun ce an dakatar da tattaunawar ce na ɗan ƙaramin lokaci, kuma za a ci gaba da ita duk da yake ba su bayyana zuwa wane lokaci ba.