Leadership News Hausa:
2025-07-25@00:39:31 GMT

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Published: 7th, June 2025 GMT

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Kungiyar ƙwallon ƙafa ta Tottenham Hotspur ta sallami kocinta Ange Postecoglu ƙasa da wata daya bayan ya lashe kofin Uefa Europa League na bana, Ange wanda ya zo Tottenham daga Celtic ya shafe shekaru biyu ya na jan ragamar kungiyar.

Shugaban Tottenham Levy ne ya bayyana wannan mataki na sallamar Ange bayan wani taro da mahukuntan ƙungiyar suka yi a ranar Juma’a, wanda ya ce hakan shi ne mafita ga ɓangarensu da kuma ɓangaren kocin wanda ya jagoranci wasanni 101 a matsayin koci.

Liverpool Sun Zama Zakaran Gasar Premier Bayan Lallasa Tottenham Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

A zahiri, alaƙar babban kocin da tawagarsa ta zama ɗaya daga cikin manyan dalilan da suka sa kocin mai shekaru 59 ya ci gaba da zama, amma kwanaki 16 kacal bayan nasarar lashe kofin Yefa Europa League a Bilbao, an kori Postecoglou shekaru biyu kacal da zuwanshi Landan.

Tottenham ta samu nasarar lashe kofin Europa League bayan da ta doke abokiyar karawarta Manchester United a wasan ƙarshe da aka buga a filin wasa na San Mames da ke birnin Bilbao, kafin zuwa Ange kungiyar dake gabascin Landan ta shafe shekaru fiye da 20 ba tare da lashe wani kofi ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Matasa 3 sun rasu yayin wanka a rafi a Bauchi

Wasu matasa uku daga ƙauyen Durum sun rasu yayin da suke wanka a wani rafi a ƙauyen Jinkiri, cikin gundumar Tirwun a Ƙaramar Hukumar Bauchi.

Matasan su ne; Habibu Mohammed mai shekaru 16, Abubakar Mohammed mai shekaru 16, da kuma Zailani Sule mai shekaru 14.

2027: Obi zai iya takara ba tare da ni ba — Datti Baba-Ahmed NEDC ta raba wa mutanen da ambaliya ta shafa kayan gini a Yobe

kakakin rundunar ’yan sandan Jihar, CSP Mohammed Ahmed Wakil, ya bayyana wa manema labarai faruwar lamarin.

Duk da ƙoƙarin da aka yi na ceto su, matasan sun rasu kafin a kai su asibiti.

Wakil, ya ce bincike ya nuna cewa matasan sun yi aikin haƙar ma’adinai, wanda daga bisani suka yanke shawarar yin wanka a rafin.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyayen mamatan.

Ya kuma ja hankalin jama’a kan muhimmancin guje wa wanka a irin waɗannan wurare masu hatsari.

CSP Wakil ya ce an miƙa wa iyayen matasan gawarwakinsu domin yi musu jana’iza, bayan da likitoci sun tabbatar da rasuwarsu.

Rundunar ta ce za ta ci gaba da wayar da kan jama’a da ɗaukar matakan kare rayuka, domin hana irin wannan mummunan lamari sake faruwa a nan gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Alakar Sin Da EU Na Bukatar Hadin Gwiwa Ba Raba-gari Ba
  • Hulk Hogan ya mutu yana da shekara 71
  • Ruwa da iska sun kashe mutum 5, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
  • Ruwa da iska sun kashe mutum, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
  • Nentawe Yilwatda ne zai zama sabon shugaban APC na kasa
  • An Kaddamar Da Bikin BIRTV2025 A Beijing
  • Matasa 3 sun rasu yayin wanka a rafi a Bauchi
  • NEDC ta raba wa mutanen da ambaliya ta shafa kayan gini a Yobe
  • Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa
  • Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa