Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu
Published: 7th, June 2025 GMT
Kungiyar ƙwallon ƙafa ta Tottenham Hotspur ta sallami kocinta Ange Postecoglu ƙasa da wata daya bayan ya lashe kofin Uefa Europa League na bana, Ange wanda ya zo Tottenham daga Celtic ya shafe shekaru biyu ya na jan ragamar kungiyar.
Shugaban Tottenham Levy ne ya bayyana wannan mataki na sallamar Ange bayan wani taro da mahukuntan ƙungiyar suka yi a ranar Juma’a, wanda ya ce hakan shi ne mafita ga ɓangarensu da kuma ɓangaren kocin wanda ya jagoranci wasanni 101 a matsayin koci.
A zahiri, alaƙar babban kocin da tawagarsa ta zama ɗaya daga cikin manyan dalilan da suka sa kocin mai shekaru 59 ya ci gaba da zama, amma kwanaki 16 kacal bayan nasarar lashe kofin Yefa Europa League a Bilbao, an kori Postecoglou shekaru biyu kacal da zuwanshi Landan.
Tottenham ta samu nasarar lashe kofin Europa League bayan da ta doke abokiyar karawarta Manchester United a wasan ƙarshe da aka buga a filin wasa na San Mames da ke birnin Bilbao, kafin zuwa Ange kungiyar dake gabascin Landan ta shafe shekaru fiye da 20 ba tare da lashe wani kofi ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
2027: Makomar Shettima a matsayin abokin takarar Tinubu na janyo cece-kuce
Shugaba Bola Tinubu ya samu goyon bayan manyan jiga-jigan jam’iyyar APC domin sake tsayawa takara a zaɓen 2027, amma sunan Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima bai fito ba yayin tattaunawar lamarin da ya haifar da tambayoyi game da makomarsa a siyasa.
Ko da yake Shettima ya halarci babban taron jam’iyyar APC na ƙasa, inda aka nuna wa Tinubu goyon baya, amma ba a ambaci sunansa ba a wajen taron.
Sabon Rikici: An kashe dan shekara 13 da wasu 3 a Filato Kwamishina ya yi murabus saboda sauya sheƙar Gwamnan Akwa IbomWannan ya sa mutane da dama suka fara tunanin ko zai dawo a matsayin mataimaki ɗan takarar shugaban ƙasa a 2027.
Wasu ’ya’yan jam’iyyar na cewa, goyon bayan Tinubu ba yana nufin goyon bayan Shettima ba.
“Zaɓi ne da ke hannun shugaban ƙasa wanda zai zaɓa mataimakinsa,” in ji Cif Sam Nkire, ɗaya daga cikin jiga-jigan jam’iyyar APC.
“Mataimakin shugaban ƙasa dole ya ci gaba da zama lafiya da mutane domin shugaba ya ci gaba da amincewa da su.”
Akwai damuwa daga ɓangaren Arewa maso Gabas, yankin Shettima, inda wasu ke buƙatar a fito a bayyana matsayin mataimakin shugaban ƙasa kafin lokacin zaɓen.
“Muna buƙatar bayani,” in ji Barrista Abdullahi Jalo.
“Shiru a kan Shettima ba abu ne da za a wuce haka kawai ba, kuma ya cancanci a yi wa yankin bayani.”
Har yanzu dai Jihar Borno ce kaɗai daga Arewa maso Gabas da ta fito fili ta nuna goyon bayan Tinubu da Shettima tare.
Masana siyasa suna cewa tarihin Tinubu na canja mataimaka a lokacin da yake gwamnan Legas, inda ya sauya mataimakin gwamna sau uku na iya sake maimaituwa a matakin ƙasa.
Daraktan Yaɗa Labaran APC, Bala Ibrahim, ya jaddada cewa goyon bayan da aka nuna wa Tinubu ya shafi ofishin shugaban ƙasa gaba ɗaya.
“Idan jam’iyya na goyon bayan shugaban ƙasa, to ba a cire mataimakinsa daga ciki ba, sai dai idan shi ya bayyana hakan da kansa.”
Sai dai rashin hoto ko sunan Shettima a cikin tallace-tallacen kamfen ɗin Tinubu da bayanan jam’iyya yana ƙara jefa shakku a zukatan wasu.
Mutane da dama a Arewa maso Gabas na jin kamar ana ƙoƙarin watsar da su, musamman ganin yadda Arewa maso Yamma ke ci gaba da riƙe manyan muƙamai a gwamnatin yanzu.
Ana sa ran za a gudanar da wani babban taro na APC a Gombe a ranar 16 ga watan Yuni don duba wannan lamari.
Masu ruwa da tsaki za su tattauna kan tikitin 2027 da kuma yiwuwar tabbatar da tikitin Tinubu da Shettima.
Amma har yanzu, tambayoyi kan makomar Shettima ba su samu amsa ba.