Leadership News Hausa:
2025-12-13@13:08:22 GMT

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Published: 7th, June 2025 GMT

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Kungiyar ƙwallon ƙafa ta Tottenham Hotspur ta sallami kocinta Ange Postecoglu ƙasa da wata daya bayan ya lashe kofin Uefa Europa League na bana, Ange wanda ya zo Tottenham daga Celtic ya shafe shekaru biyu ya na jan ragamar kungiyar.

Shugaban Tottenham Levy ne ya bayyana wannan mataki na sallamar Ange bayan wani taro da mahukuntan ƙungiyar suka yi a ranar Juma’a, wanda ya ce hakan shi ne mafita ga ɓangarensu da kuma ɓangaren kocin wanda ya jagoranci wasanni 101 a matsayin koci.

Liverpool Sun Zama Zakaran Gasar Premier Bayan Lallasa Tottenham Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

A zahiri, alaƙar babban kocin da tawagarsa ta zama ɗaya daga cikin manyan dalilan da suka sa kocin mai shekaru 59 ya ci gaba da zama, amma kwanaki 16 kacal bayan nasarar lashe kofin Yefa Europa League a Bilbao, an kori Postecoglou shekaru biyu kacal da zuwanshi Landan.

Tottenham ta samu nasarar lashe kofin Europa League bayan da ta doke abokiyar karawarta Manchester United a wasan ƙarshe da aka buga a filin wasa na San Mames da ke birnin Bilbao, kafin zuwa Ange kungiyar dake gabascin Landan ta shafe shekaru fiye da 20 ba tare da lashe wani kofi ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Matatar man Dangote ta rage farashin fetur zuwa N699

Matatar man Dangote ta sake rage farashin man fetur ɗin da take sayar da man, inda ta rage farashin man fetur ɗin daga Naira 828 zuwa Naira 699 kan kowace lita.

Bayanan farashin da aka wallafa a shafin  kasuwancin farashin man fetur a Petroleumprice.ng a ranar Juma’a sun nuna cewa matatar ta aiwatar da wani bita na baya-bayan nan, inda ta rage farashin man da N129 a kowace lita – ragin kashi 15.58 cikin 100.

Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai Dan sanda ya yi batan dabo a bakin aikinsa a Katsina

Wani jami’in matatar man da ya zanta da manema labarai bisa sharaɗin sakaya sunansa saboda ba shi da izinin yin tsokaci a bainar jama’a, shi ma ya tabbatar da yin ragin.

Ya ce, matatar man ta rage farashin man fetur zuwa N699 kowace lita.

Sabon farashin ya fara aiki ne daga ranar 11 ga watan Disamba, 2025, wanda ya yi daidai da farashin man fetur karo na 20 da matatar man ta sanar a bana.

Ragi na baya-bayan nan ya zo ne kwanaki biyar bayan shugaban matatar, Aliko Dangote ya jaddada ƙudirinsa na ganin an tabbatar da farashin man fetur a cikin gida cikin “madaidaicin farashi a kasuwanni” duk kuwa da taɓarɓarewar da ake samu a duniya da fasaƙwaurin da ake yi a kan iyakokin Najeriya.

Da yake bayani bayan ganawar sirri da shugaban Najeriya, Bola Tinubu a ranar 6 ga watan Disamba, Dangote ya ce farashin zai ci gaba da faɗuwa yayin da matatar man ke ƙara yawan kayan da ake fitarwa da kuma yin gogayya kai tsaye da kayayyakin da ake shigowa da su daga ƙasashen waje.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe
  • Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya
  • Matatar man Dangote ta rage farashin fetur zuwa N699
  • Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda
  • Dan sanda ya yi batan dabo a bakin aikinsa a Katsina
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano
  • Osimhen Ya Lashe Kyautar Gwarzon Dan Wasan Kwallon Kafa Na Bana A Kasar Turkiyya
  • Kasashen Nijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Tsaro Ta Shekaru 5 
  • Najeriya za ta buga wasan sada zumunta da Masar kafin fara gasar AFCON ta 2025
  • Real Madrid  za ta ɓarje gumi da Manchester City a Santiago