HausaTv:
2025-06-12@05:57:42 GMT

Gidauniyar Hind Rajab ta kai karar Isra’ila kan harin jirgin ruwan Madleen

Published: 10th, June 2025 GMT

Gidauniyar Hind Rajab (HRF), mai rajin kare hakkin Falasdinawa, ta shigar da kara kan laifukan yaki bayan farmakin da sojojin ruwan Isra’ila suka kai kan jirgin ruwan agaji na Birtaniya Madleen a ruwan kasa da kasa a yammacin Lahadi.

Koken dai ya shafi rundunar sojin ruwa ta Isra’ila Shaytet 13 da kwamandan ta, Vice Admiral David Saar Salama.

Gidauniyar ta HRF ta yi kira da a gaggauta sakin masu fafutuka 12 da ake tsare da su, ciki har da mai fafutukar kare muhalli Greta Thunberg, dan wasan kwaikwayo Liam Cunningham, da Rima Hassan ta faransa, wadanda ke hannun Isra’ila.

Jirgin ruwan na Madleen, na kungiyar Freedom Flotilla Coalition, na dauke da kayayyakin jinya, da abinci, da madarar jarirai, da sauran kayan agaji da aka nufi zuwa Gaza a lokacin da aka kama shi fiye da mil 60 a tekun ruwa.

Madleen, wanda ya tashi daga Sicily, an dora masa alhakin isar da kayayyakin jin kai zuwa Gaza wanda Isra’ila ta yi kawanya.

Sojojin Isra’ila sun shiga cikin jirgin, sun kame fasinjoji tare da kwace kayan agajin.

Dama Irin wannan lamari ya faru a watan Mayun 2025, lokacin da jiragen Isra’ila marasa matuka suka kai hari kan wani jirgin ruwa dauke da Greta Thunberg a gabar tekun Malta.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila ta sake kashe Falasdinawa a wurin rabon tallafi

Bayanai daga Falasdinu na cewa akalla mutum 20 ne sukayi shahada a wani sabon harin da sojojin Isra’ila suka kai a lokacin da ake rabon abinci a Gaza.

Shaidun gani da ido sun ce sojojin Isra’ila sun bude wuta da safiyar Talatar nan, kan Falasdinawa da za su karbi kayayyaki a tsakiyar Gaza a wani wuri da ke karkashin gidauniyar agaji ta Gaza (GHF).

Jami’an Falasdinawa sun kara da cewa sama da mutane 120 ne suka jikkata a harin na Isra’ila.

Harin na baya-bayan nan ya zo ne sa’o’i bayan da sojojin Isra’ila suka kashe Falasdinawa 14 da suka taru a wajen wata cibiyar GHF da ke kudancin Rafah.

Kisan na yau ya sanya adadin wadanda sukayi shahada a wajen rabon abinci a Gaza sanadin hare-haren Isra’ila zuwa 110 tun ranar 27 ga watan Mayu, a tsarin rabon abincin na GHF da ke samun goyon bayan Isra’ila da Amurka.

Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa ne ke sukan tsarin rabon tallafin wanda wasu ke dangantawa da tarkon mutuwa.

Halin da ake ciki na jin kai a Gaza ya kai intaha inda kungiyoyi musamman MDD ke bayyana shi da mafi muni a duniya.

Tun bayan fara yakin kisan kare dangi da Isra’ila ta kaddamar a ranar 7 ga Oktoba, 2023, adadin Falasdinawa da sukayi shahada ya kai 54,927, yawancinsu mata da kananan yara, sannan wasu kusan 126,615 sun jikkata.

A watan Nuwamba 2024, Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ta ba da sammacin kama Firayim Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da tsohon ministansa na soja Yoav Gallant, bisa zarginsu da laifukan yaki da cin zarafin bil’adama a Gaza.

Haka zalika kuma ana zargin gwamnatin Isra’ila da kisan kare dangi a gaban kotun kasa da kasa ta ICJ saboda ta’addancin da ta aikata a zirin Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu ta yi fatali da bukatar Akpabio, ta umarce shi ya biya Natasha N100,000
  • A hanzarta kwangilar yashe Madatsar Ruwa ta Alau — Gwamnatin Borno
  • A hanzarta kwangilar yashe Madatsar Ruwa ta Alou — Gwamnatin Borno
  • IRGC : A yanzu makamman Iran masu linzami zasu iya harin Isra’ila daidai inda ake so
  • Isra’ila ta sake kashe Falasdinawa a wurin rabon tallafi
  • Al’ummomi Daga Sassan Duniya Suna Yin Tofin Allah Tsine Kan Sace Masu Fafatuka A Kan Hanyarsu Ta Zuwa Gaza 
  • Isra’ila ta ƙwace jirgin ruwa a hanyar kai agaji Gaza
  • Wasu Jiragen Ruwa Na  Ceto Da Jin Kai  Sun  Tashi Daga Tunisiya Zuwa Gabar Ruwan Gaza
  • HKI Ta Kaiwa Jirgin Ruwan Masu Rajin Kare Hakkin Mutanen Gaza Na Jinkai Wato Madleen