IRGC : Iran a shirye take na tunkarar duk wani yanayi
Published: 12th, June 2025 GMT
Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya bayyana cikakken shirin Iran na tunkarar duk wani mataki na wuce gona da iri a daidai lokacin da ake ci gaba da fuskantar barazanar daukar matakin soji kan kasar.
Manjo Janar Hossein Salami ya bayyana hakan ne yau Alhamis, yayin da rahotanni ke nuni da cewa, Amurka ta sanya ofisoshin jakadancinta da sansanonin sojinta da ke yammacin Asiya cikin shirin ko-ta-kwana saboda fargabar yiwuwar kai wa Iran hari.
“A wasu lokuta makiya suna yi mana barazana da daukar matakin soji, mun sha bayyanawa, kuma muna maimaitawa a yau, cewa mun shirya tsaf don fuskantar duk wani yanayi,” in ji shi.
“Muna da kwarewa, mun karfafa karfinmu tare da samar da dabaru a cikin tsare-tsarenmu.
Muna sa ido sosai kan sojojin abokan gaba kuma mun aiwatar da shirye-shiryenmu.” Inji shi.
Har ila yau babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci ya gargadi makiya game da duk wani gigi, ya kuma shawarce su da su yi la’akari da illolin da ayyukansu zasu haifar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
A Bai Wa Kudu Tikitin Takara A 2027 Ko PDP Ta Ruguje – Wani Jigo A PDP
Ya ƙara da cewa babu wani ɗan siyasa da zai iya lashe zaɓe shi kaɗai.
“Ku bai wa Kudu tikitin, ku ga sakamako. Amma idan PDP ta ci gaba da tafiya a kan wannan kuskure, to, za ta fuskanci babbar matsala a 2027,” Yusuf ya bayyana.
Ya kuma bayyana cewa Atiku Abubakar ba ɗa jam’iyyar PDP ba ne a yanzu, yana tare da wata sabuwar tafiyar haɗin gwiwa ta siyasa.
Yusuf ya ɗora alhakin faɗuwar jam’iyyar a zaɓen 2023 kan rashin kyakkyawan shugabanci da kuma rabon tikiti ba bisa ƙa’ida ba.
Ya ce rikicin cikin gida da kuma gazawar PDP wajen kulawa da ‘yan Kudu ne suka sa jam’iyyar ta faɗi.
Ya kuma nuna takaicinsa game da sauya sheƙar Gwamnan Jihar Delta na baya, Ifeanyi Okowa, zuwa jam’iyyar APC, yana mai cewa hakan na nuna cewa PDP ta kasa tsara kamfen ɗinta yadda ya dace.
Ya buƙaci shugabannin PDP da su daina dogaro da tsofaffi a siyasa, su mayar da hankali wajen gina sabuwar amana da haɗin kai, musamman a yankin Kudu.
A cewarsa, adalci, haɗin gwiwa, da sake gina jam’iyya su ne kawai hanyar da PDP za ta iya dawowa da ƙarfi a zaɓen 2027.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp