An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari
Published: 12th, June 2025 GMT
Babban baturen ’yan sanda na birnin Ahmedabad da ke ƙasar Indiya ya bayyana cewa, an ciro gawar mutane sama da 200 na fasinjojin jirgin Air India da ya yi hatsari a yau Alhamis.
Babban jami’in ɗan sandan ya bayyana hakan ne a matsayin bayani na baya-bayan nan kan hatsarin jirgin, wanda ya rikito ƙasa jim kadan bayan tashi, kan hanyarsa ta zuwa birnin London na Birtaniya.
Shugaban hukumar kula da sufurin jiragen sama na Indiya ya ce jirgin na ɗauke ne da mutum 242, kuma akasarinsu Indiyawa ne.
Fasinjojin jirgin Indiya da yawa sun mutu a hatsarin
A cewar Kamfanin Dillancin Labarai na AP ya ambato shugaban ƴan sanda na birnin Ahmedabad na cewa akwai yiwuwar babu wanda ya tsira da ransa a hatsarin da jirgin sama mallakin kamfanin sufuri na India Air ya faru yau a birnin.
Ya bayyana hakan ne yayin da yake bayani kan hatsarin jirgin da ke kan hanyarsa ta zuwa birnin London na ƙasar Birtaniya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Birtaniya
এছাড়াও পড়ুন:
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik November 2, 2025
Daga Birnin Sin An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu November 2, 2025
Daga Birnin Sin Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya November 1, 2025