Aminiya:
2025-09-17@23:10:37 GMT

Gwamnan Kebbi ya bai wa ’yan kasuwar katako tallafin ibtila’in gobara

Published: 10th, June 2025 GMT

Gwamnan Kebbi, Dakta Nasir Idris (Ƙauran Gwandu) ya jajanta wa al’ummar kasuwar katako ta bayan kara da ke Birnin Kebbi bisa ibtila’in gobara da ta auka musu.

Mataimakin Gwamnan, Sanata Umar Abubakar Tafida ne ya wakilci gwamnan a yayin ziyarar jaje da ya kai wa ’yan kasuwar da abin ya shafa.

A saurari sauyin da za mu yi wa ɓangaren man fetur a Nijeriya — Dangote NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Magance Matsalar Kwacen Waya

A lokacin da ya zagaya domin duba irin ɓarnar da wutar ta yi a kasuwar, Mataimakin Gwamna ya yi kira da su mayar da lamarin ga Allah da kuma ɗaukar wannan ibtila’in a matsayin jarabawa daga gare Shi.

Haka kuma, ya miƙa wa ’yan kasuwar gudumawar Naira miliyan goma da gwamnan ya bayar a matsayin tallafi na farko domin rage musu raɗadin wannan ibtila’in.

Kazalika, ya bayyana cewar gwamnati za ta yi duk mai yiyuwa wajen taimaka wa ’yan kasuwar domin ci gaba da sana’ar su bayan an kammala ɗaukar bayanan da suka dace a kasuwa.

Shugaban ’yan kasuwar, Alhaji Bello Ɗan-Sambo, ya yi godiya ga gwamnan da mataimakinsa bisa ziyarar jaje da aka kai musu.

Haka kuma, ya yi godiya ga gwamnatin bisa gudunmawar Naira miliyan goma da ya bayar ga ’yan kasuwar da abin ya shafa.

Aminiya ta ruwaito cewa a ranar Lahadin da ta gabata ce gobara ta laƙume kasuwar katako da ke bayan kara a Jihar Kebbi.

Shaidu sun ce gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 5:00 na Asuba bayan dawo da wutar lantarki, inda ta ƙone shaguna kimanin 30.

Aƙalla ’yan kasuwa tara ne gobarar ta shafa wacce ta laƙume dukiyar da ta kai kimanin Naira miliyan dari da casa’in.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Jihar Kebbi Kasuwar Katako yan kasuwar

এছাড়াও পড়ুন:

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

An garzaya da ita asibiti, amma daga baya likitoci suka tabbatar da mutuwarta.

’Yansanda sun kama Bosede kuma suna bincike a kan lamarin.

Kakakin rundunar, DSP Olusola Ayanlade, ya ce za su tabbatar da adalci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Ya Ba Da Tallafin Kayayyakin Aiki Ga Cibiyoyin Lafiya A Kirikasamma
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja