Aminiya:
2025-07-27@10:30:46 GMT

Gwamnan Kebbi ya bai wa ’yan kasuwar katako tallafin ibtila’in gobara

Published: 10th, June 2025 GMT

Gwamnan Kebbi, Dakta Nasir Idris (Ƙauran Gwandu) ya jajanta wa al’ummar kasuwar katako ta bayan kara da ke Birnin Kebbi bisa ibtila’in gobara da ta auka musu.

Mataimakin Gwamnan, Sanata Umar Abubakar Tafida ne ya wakilci gwamnan a yayin ziyarar jaje da ya kai wa ’yan kasuwar da abin ya shafa.

A saurari sauyin da za mu yi wa ɓangaren man fetur a Nijeriya — Dangote NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Magance Matsalar Kwacen Waya

A lokacin da ya zagaya domin duba irin ɓarnar da wutar ta yi a kasuwar, Mataimakin Gwamna ya yi kira da su mayar da lamarin ga Allah da kuma ɗaukar wannan ibtila’in a matsayin jarabawa daga gare Shi.

Haka kuma, ya miƙa wa ’yan kasuwar gudumawar Naira miliyan goma da gwamnan ya bayar a matsayin tallafi na farko domin rage musu raɗadin wannan ibtila’in.

Kazalika, ya bayyana cewar gwamnati za ta yi duk mai yiyuwa wajen taimaka wa ’yan kasuwar domin ci gaba da sana’ar su bayan an kammala ɗaukar bayanan da suka dace a kasuwa.

Shugaban ’yan kasuwar, Alhaji Bello Ɗan-Sambo, ya yi godiya ga gwamnan da mataimakinsa bisa ziyarar jaje da aka kai musu.

Haka kuma, ya yi godiya ga gwamnatin bisa gudunmawar Naira miliyan goma da ya bayar ga ’yan kasuwar da abin ya shafa.

Aminiya ta ruwaito cewa a ranar Lahadin da ta gabata ce gobara ta laƙume kasuwar katako da ke bayan kara a Jihar Kebbi.

Shaidu sun ce gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 5:00 na Asuba bayan dawo da wutar lantarki, inda ta ƙone shaguna kimanin 30.

Aƙalla ’yan kasuwa tara ne gobarar ta shafa wacce ta laƙume dukiyar da ta kai kimanin Naira miliyan dari da casa’in.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Jihar Kebbi Kasuwar Katako yan kasuwar

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Wannan yana cikin wani tsari na noma da aka kirkiro musamman don masu bukata ta musamman domin su dogara da kansu maimakon rokon hatsi ko neman taimako.

Wannan yana cikin wani tsari na noma da aka kirkiro musamman don masu bukata ta musamman domin su dogara da kansu maimakon rokon hatsi ko neman taimako.

Wakilinmu ya ziyarcj wata kebabbiyar gona dake cikin garin Kaduna, inda gungun wasu manoma da ke fama da lalurori daban-daban irin su makanta da gurguntaka da kurma, suka rungumi sabbin dabarun noma na zamani domin tallafawa rayuwarsu, musamman a wannan damina da aka shiga.

Gonakin da wadanda makafi da guragu ne suke nomawa a duk shekara Sun bayyana cewa suna gudanar da nomansu ne ba tare da wata gudummawa daga gwamnati ba kama da samar musu da takin zamani da sauran kayan noma kamar yadda ake tallafawa Masu lafiya.

A zantawarsa da wakilinmu a cikin gonarsa, Mista William Makiya, wanda ke fama da matsalar gani (makaho), yana noma da huda domin ciyar da iyalinsa. Ya bayyana cewa:

“Ba na gani da idona. Dalilin da yasa nake yin noma shine domin ciyar da iyalina. Ba na yin bara kuma bana san yin bara kwata-kwata rayuwata. Ba na kaunar bara.”

William ya kara da cewa yana jin dadin aikin noma, kuma yana taimakawa makwabtansa masu lafiya da kayan abinci daga gonarsa. Wannan yana karfafa zumunci da hadin kai tsakaninsa da sauran al’umma da suke zaune tare a cikin muhalli daya.

Ya ce:“Da galma nake yin wannan noma. Ina amfani da fatanya da sauran kayan huda wajen noma da kuma cire ciyawa a gonaki.”

Ya ci gaba da cewa gonarsa tana da layukan shuka wanda yake amfani da su wajen shuka wake, dankalin hausa, gyada, da kayan lambu irin su tumatur da kubewa.

A kowace shekara, jajirtattun manoma masu bukata ta musamman ne ke amfani da wadannan filayen noma domin ciyar da kansu, kamar yadda wani matashi mai lalurar kafa Mai Suna Joshua Matthew, ya bayyana cewa Shi ma yana noma da huda a gonarsa.

“Abin da ya kamata a sani shi ne, ni ina noma da huda sosai domin ciyar da iyalina. Ina noma masara da shinkafa da sauran kayayyakin abinci domin rage tsadar rayuwa.”

Joshua ya ce duk da cewa ba shi da kafa, yana zaune yana jan jikinsa domin yin noma da cire ciyawa da sauran ayyukan noma. Ya tabbatar da cewa ya dade yana wannan aiki, kuma babu wahala kamar yadda mutane ke tunani.

Ya jaddada bukatar gwamnati ta tallafa musu domin su zama masu dogaro da kansu.

Duk da karancin ruwan sama a bana, wadannan manoma ba su karaya ba. Sun ci gaba da aiki tukuru a gonakinsu, suna amfani da dabarun noma na zamani domin tabbatar da samun abinci mai yawa da inganci.

Babu shakka, wadannan manoma suna gudanar da aikin noma ta hanyar wani tsarin hada kowa da kowa musamman masu nakasa cikin harkar noma domin yakar yunwa da talauci a Nijeriya. Wannan tsarin na “inclusibe smart farming” ya fara haifar da nasarori, a cewar Kwamared Rilwani Abdullahi, shugaban kungiyar masu bukata ta musamman a Nijeriya.

Ya ce:“Wannan wani yunkuri ne na zama masu dogaro da kai. Saboda haka, muna kira ga hukumomi da su tashi tsaye wajen tallafawa wadannan manoma, da kuma tabbatar da cewa ana sanya su a cikin jerin manoman da ake tallafawa a duk lokacin da ake rabon takin zamani.”

Yanzu haka dai, wadannan gwarazan manoma sun dukufa sosai cikin harkar noma domin ciyar da kansu maimakon barace-barace. Sai dai, sun koka kan yadda ake rarraba takin zamani ba tare da an tuna da su ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
  • Tallafin Lafiya: Ƙungiyar Rotary Ta Raba Kayan Haihuwa kyauta Ga Mata Masu Juna Biyu  A Kaduna
  • NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Naira Biliyan 3.5 Wajen Gina Shaguna A Farm Centre
  • Naira: Kotu ta yanke wa Hamisu Breaker da G-Fresh hukunci ɗaurin wata 5
  • Wulaƙanta Naira: Kotu ta bayar da belin Hamisu Breaker da G-Fresh
  • Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah
  • ‘Yan Majalisa Sun Zargi Hukumomin Gwamnati Da Wawure Sama Da Naira Biliyan 103.8
  • Ina Karanta Rantsuwar Da Na Yi A Kullum Don Tuna Nauyin Da Ke Kaina-Gwamna Namadi
  • Syria: Mutane Da Dama Sun Mutu Da Kuma Jikkata Sanadiyyar Gobara A Rumbun Ajiyar Makamai