Aminiya:
2025-06-14@02:10:18 GMT

Gwamnan Kebbi ya bai wa ’yan kasuwar katako tallafin ibtila’in gobara

Published: 10th, June 2025 GMT

Gwamnan Kebbi, Dakta Nasir Idris (Ƙauran Gwandu) ya jajanta wa al’ummar kasuwar katako ta bayan kara da ke Birnin Kebbi bisa ibtila’in gobara da ta auka musu.

Mataimakin Gwamnan, Sanata Umar Abubakar Tafida ne ya wakilci gwamnan a yayin ziyarar jaje da ya kai wa ’yan kasuwar da abin ya shafa.

A saurari sauyin da za mu yi wa ɓangaren man fetur a Nijeriya — Dangote NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Magance Matsalar Kwacen Waya

A lokacin da ya zagaya domin duba irin ɓarnar da wutar ta yi a kasuwar, Mataimakin Gwamna ya yi kira da su mayar da lamarin ga Allah da kuma ɗaukar wannan ibtila’in a matsayin jarabawa daga gare Shi.

Haka kuma, ya miƙa wa ’yan kasuwar gudumawar Naira miliyan goma da gwamnan ya bayar a matsayin tallafi na farko domin rage musu raɗadin wannan ibtila’in.

Kazalika, ya bayyana cewar gwamnati za ta yi duk mai yiyuwa wajen taimaka wa ’yan kasuwar domin ci gaba da sana’ar su bayan an kammala ɗaukar bayanan da suka dace a kasuwa.

Shugaban ’yan kasuwar, Alhaji Bello Ɗan-Sambo, ya yi godiya ga gwamnan da mataimakinsa bisa ziyarar jaje da aka kai musu.

Haka kuma, ya yi godiya ga gwamnatin bisa gudunmawar Naira miliyan goma da ya bayar ga ’yan kasuwar da abin ya shafa.

Aminiya ta ruwaito cewa a ranar Lahadin da ta gabata ce gobara ta laƙume kasuwar katako da ke bayan kara a Jihar Kebbi.

Shaidu sun ce gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 5:00 na Asuba bayan dawo da wutar lantarki, inda ta ƙone shaguna kimanin 30.

Aƙalla ’yan kasuwa tara ne gobarar ta shafa wacce ta laƙume dukiyar da ta kai kimanin Naira miliyan dari da casa’in.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Jihar Kebbi Kasuwar Katako yan kasuwar

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano za ta binciki musabbabin gobarar kasuwar Farm Center

Gwamnatin jihar Kano ta kafa wani kwamitin da zai binciki musabbabin gobarar da ta tashi a kwanan nan a kasuwar wayoyin hannu ta Farm Center da ke jihar.

A ranar Juma’ar da ta gabata ce dai gobara ta tashi a kasuwar wacce aka yi kiyasin ta kone shaguna sama da 300 tare da janyo wa ’yan kasuwa asarar miliyoyin Naira.

Za a dauke wa jihohin Arewa maso Gabas wutar lantarki na tsawon kwana 4 Kotu ta yi fatali da bukatar Akpabio, ta umarce shi ya biya Natasha N100,000

Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Umar Ibrahim ne ya rantsar da kwamitin a madadin Gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf.

Kwamitin dai kasance karkashin jagorancin Kwamishinan Ayyuka na Musammanna jihar, Alhaji Umar Ibrahim kuma yana da wakilai daga hukumomin gwamnati da jami’an tsaro da ma manyan masu ruwa da tsaki a harkokin kasuwanci.

An dai dora wa kwamitin alhakin gano ainihin abin da ya haddasa gobarar sannan ya gano yawan asarar da aka tafka da kuma bayar da shawarwarin kauce wa sake aukurar irin ta a nan gaba.

Sakataren gwamnatin dai ya hori kwamitin da yin aiki tukuru wajen ganin ya sauke nauyin da aka dora masa.

Ya kuma yi kira ga kungiyoyi da daidaikun jama’a masu hannu da shuni da su taimaka wa ’yan kasuwar da tallafi ta hanyar asusun da gwamnati ta tanada, yana mai ba da tabbacin cewa za a yi adalci wajen rabon tallafin da aka tara.

Ana sa ran kwamitin zai kammala aikinsa tare da mika rahotonsa cikin mako daya daga kaddamar da shi.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi
  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai
  • ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2
  • Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba
  • Gobara Ta Ƙone Wani Gidan Mai A Legas
  • Mokwa: Zulum ya kai ziyarar jaje Neja, ya bayar da tallafin N300m
  • Ana zargin uwa da kashe ’yarta kan Naira 100 a Zariya
  • Gwamnatin Kano za ta binciki musabbabin gobarar kasuwar Farm Center