Aminiya:
2025-11-02@06:26:19 GMT

Gwamnan Kebbi ya bai wa ’yan kasuwar katako tallafin ibtila’in gobara

Published: 10th, June 2025 GMT

Gwamnan Kebbi, Dakta Nasir Idris (Ƙauran Gwandu) ya jajanta wa al’ummar kasuwar katako ta bayan kara da ke Birnin Kebbi bisa ibtila’in gobara da ta auka musu.

Mataimakin Gwamnan, Sanata Umar Abubakar Tafida ne ya wakilci gwamnan a yayin ziyarar jaje da ya kai wa ’yan kasuwar da abin ya shafa.

A saurari sauyin da za mu yi wa ɓangaren man fetur a Nijeriya — Dangote NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Magance Matsalar Kwacen Waya

A lokacin da ya zagaya domin duba irin ɓarnar da wutar ta yi a kasuwar, Mataimakin Gwamna ya yi kira da su mayar da lamarin ga Allah da kuma ɗaukar wannan ibtila’in a matsayin jarabawa daga gare Shi.

Haka kuma, ya miƙa wa ’yan kasuwar gudumawar Naira miliyan goma da gwamnan ya bayar a matsayin tallafi na farko domin rage musu raɗadin wannan ibtila’in.

Kazalika, ya bayyana cewar gwamnati za ta yi duk mai yiyuwa wajen taimaka wa ’yan kasuwar domin ci gaba da sana’ar su bayan an kammala ɗaukar bayanan da suka dace a kasuwa.

Shugaban ’yan kasuwar, Alhaji Bello Ɗan-Sambo, ya yi godiya ga gwamnan da mataimakinsa bisa ziyarar jaje da aka kai musu.

Haka kuma, ya yi godiya ga gwamnatin bisa gudunmawar Naira miliyan goma da ya bayar ga ’yan kasuwar da abin ya shafa.

Aminiya ta ruwaito cewa a ranar Lahadin da ta gabata ce gobara ta laƙume kasuwar katako da ke bayan kara a Jihar Kebbi.

Shaidu sun ce gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 5:00 na Asuba bayan dawo da wutar lantarki, inda ta ƙone shaguna kimanin 30.

Aƙalla ’yan kasuwa tara ne gobarar ta shafa wacce ta laƙume dukiyar da ta kai kimanin Naira miliyan dari da casa’in.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Jihar Kebbi Kasuwar Katako yan kasuwar

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Bauchi na neman ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi 29

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya rattaba hannu kan sabuwar dokar da ta ƙirƙiri ƙarin ƙananan hukumomi 29 a jihar.

Wata takarda da Aminiya ta samu ta nuna cewa Mukaddashin Mataimakin Magatakarda na Majalisar Dokokin Jihar Bauchi, Musa Yerima, ya tura wannan ƙuduri zuwa Kwamitin Gyaran Kundin Tsarin Mulki, yana neman amincewar Majalisar Tarayya domin tabbatar da dokar a cikin gyaran kundin tsarin mulki da ake yi.

Tinubu ya ƙirƙiri sabon harajin da zai iya ƙara N100 a kan kowacce litar man fetur Zargin Kisan Kiristoci: ’Yan majalisar Amurka sun yi amfani da bayanai marasa tushe — Gwamnati

A halin yanzu, Jihar Bauchi na da ƙananan hukumomi 20 da kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 ya amince da su.

Da ƙarin waɗannan 29 da ake nema, jihar da ke da kimanin mutane miliyan 10 za ta samu jimillar ƙananan hukumomi 49 ke nan.

A cikin wasikar da Mataimakin Magatakarda ya aike wa Sanata Barau Jibrin, Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Duba Kundin Tsarin Mulki, ya ce: “Ina farin cikin sanar da ku cewa Majalisar Dokokin Jihar Bauchi ta amince da dokar da za ta ba da damar ƙirƙirar ƙananan hukumomi 29 a Bauchi, 2025.”

“Waɗannan ƙananan hukumomi ba za su fara aiki ba sai Majalisar Tarayya ta amince da dokar da za ta tabbatar da sunayen su kamar yadda Sashe na 8(5) na Kundin Tsarin Mulki na 1999 ya tanada.

“Na kwatanta wannan bugun da dokar da Majalisa ta amince da ita, kuma na tabbatar da cewa wannan kwafi daidai ne da dokar da aka amince da ita,” in j wasikar.

Sunayen sabbin ƙananan hukumomin da ake son kirkira sun haɗa da: Balma, Bauchi ta Gabas, Bauchi ta Yamma, Beshongo, Bula, Burra, Chinade, Dagauda/Jalam da Disina.

Sauran su ne: Dogon Jeji/Jurara, Dass ta Yamma, Gadau, Galambi, Ganjuwa ta Gabas, Girawa, Gololo, Gwana, Isawa, Jama’a, Kankara, Lame, Lere, Madara, Sade, Sakuwa, Saye, Udubo, Yankari da Zungur.

Hedikwatocinsu sun haɗa da: Nasaru, Cibiyar Mata, Miri, Beni, Bununu, Chinade, Dagauda, Disina, Dogon Jeji, Lukshi, Gadau, Kangere, Faggo, Gololo, Futuk, Isawa, Nabordo, Akuyam, Karkara, Lame, Lere, Madara, Sade, Sakuwa, Hardawa, Udubo, Yelwan Duguri da Liman Katagum.

Yerima ya ƙara da cewa: “Wannan dokar an tura ta zuwa Shugaban Kwamitin Haɗin Gwiwa na Duba Kundin Tsarin Mulki na Majalisar Tarayya domin ci gaba da matakan da suka dace.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi
  • An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara
  • Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja
  • Gwamnan Bauchi na neman ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi 29
  • Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II
  • Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II