Ministan Leken Asiri Na Iran Ya Yi Karin Bayani Kan Nasarar Samun Bayan Tsaron HKI
Published: 9th, June 2025 GMT
Ministan leken asiri na kasar Iran ya ce asiran tsaron HKI da suka shiga hannun ma’aikatansa sun shafi makaman nukliya na HKI kuma sun nuna kwarewar da jami’an leken asirin kasar suke da shi.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa wannan bayanan zasu taimakawa sojojin JMI wajen sanin wuraren da zasu kai hare hare a duk lokacinda yake ya barke tsakanin Iran da haramtacciyar kasar, na makamai da kuma na yanar gizo.
Labarin ya kara da cewa da jami’an ma’aikatar hukumar leken asiri suka yi kama daga daukar ma’aikatan da suka dace da yin hakan da dabar barun da suke yi amfani da su don kaiwa da bayan da suke bukata ya nuna irin koreawarsu a wannan aikin.
Sannan daga cikin muhimman bayanan da suka samu sun hada da na makaman nukliyar haramtacciyar kasar da kuma dangantakanta da Amurka da kuma kasashen turai rawar da wadan nan kasashe suka taka a karfafa HKI kan makamanta na kissan kaere dangi.
Ministan ya kammala da cewa bayanan da muka samu suna da muhimmanci haka ma hanyar da muka bi muka kai ga bayanan suna da muhimmanci.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
HKI Ta Kaiwa Jirgin Ruwan Masu Rajin Kare Hakkin Mutanen Gaza Na Jinkai
Wadanda suka shirya jirgin agaji zuwa Gaza mai suna Madleen sun bada sanarwan cewa HKI kai farmaki kan jirgin a safiyar yau Litinin.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa jami’an tsaron HKI sun kaiwa jirgin Madleen hare-hare a safiyar yau Litinin kafin iasar Jirgin agajin zuwa gabar tekun Medeterania a gaza.
Labarin ya kara da cewa Thiago Avila, dan rajin kare hakkin bil’adama daga kasar Brazil a cikin Jirgin ya bayyana cewa sojojin yahudawan sun yiwa jirgin kofar rago . Y ace sojojin ruwa na HKI sun kaiwa jirgin agaji ” Madleen farmakai. Jirgi wanda yake kokarin keta kofar ragon da HKI ta yi wa Gaza tun shekara 2006.
Labarin ya kara da cewa sojojin yahudawan sun kama masu rajen kare hakkin mutanen Gaza, dake cikin jirgin ruwa na Madleen saboda an daina jinn duriyarsu.
Daga cikin wadanda suke cikin wannan jirgin dai, wadanda kuma suke tsare a hannun jami’an tsaron HKI sun hada da Greta Thunberg mai rajin kare yanayi, sannan mutane 12 wadanda suke rajin kare mutanen Gaza ta hanyar Jirgin Madleen, da kuma
Sai kuma Liam Cunningham da Rima Hassan, yan majalisar dokokin Taarayyar Turai daga kasar faransa kuma yan asalin kasar Falasdinu. Labarin yace LIMA ta yada sautin da karar jiniyar da sojojin yahudawan suka kunna a lokacin kai masu hari.
Kamfanin dillancin labaran AFP na kasar Faransa ya nakalto Mahmood Abu-Odeh dan jarida wanda yake bin jirin ceton na Madleen daga kasar Jamus ya bayyana cewa an kama wadanda suke jirgin.