Matawalle ya yi wa Gwamna Lawal da wasu tayin shiga APC
Published: 8th, June 2025 GMT
Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya buƙaci Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, da ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC mai mulki.
Matawalle ya yi wannan kira ne a ranar Asabar, a garinsu Maradun, yayin da dubban magoya bayansa suka kai ziyarar gaisuwar Sallah.
Sallah: Gwamnatin Sakkwato ta bai wa kowane Alhaji kyautar N450,000 Gwamnatin Tarayya na shirin farfaɗo da kamfanin ƙarafa na AjaokutaMatawalle, wanda shi ne tsohon gwamnan Jihar Zamfara, ya ce APC jam’iyya ce ta mutanen kirki da masu kishin ƙasa.
Ya ce maimakon a ci gaba da takun-saka tsakanin gwamnati da ’yan adawa, zai fi kyau Gwamna Dauda ya fito fili ya rungumi jam’iyyar da ke da madafun iko domin ci gaban jihar da ƙasar gaba ɗaya.
“Idan Gwamna Dauda na da niyyar kawo ci gaba musamman a fannin tsaro da zaman lafiya, babu laifi ya zo ya haɗu da sauran ’yan kwamitin ci gaba a APC,” in ji Matawalle.
Matawalle, ya jaddada cewa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu na ƙoƙari wajen samar da zaman lafiya da ci gaban ƙasa, kuma yana buƙatar goyon bayan gwamnonin jihohi da sauran shugabanni don cimma nasara.
A baya-bayan nan, wasu ’yan siyasa daga jam’iyyun adawa da dama sun sauya sheƙa zuwa APC.
Sun bayyana cewa suna son su haɗa kai da Gwamnatin Tarayya wajen samun mafita ga matsalolin da ƙasar ke fuskanta.
Wannan na ƙara wa APC ƙarfi a jihohi da dama, ciki har da Zamfara.
Kiran da Matawalle ya yi wa Gwamna Dauda Lawal da wasu shugabannin adawa na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyyar APC ke ƙara karɓar sabbin mambobi daga jam’iyyun adawa, a wani yunƙuri na ƙarfafa tsarin mulki.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamna Lawal matawalle Sauya Sheƙa Tsaro Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Rasha Ta Kai Wasu Munanan Hare-Hare Kan Kasar Ukraine Tare Da Janyo Mata Munanan Barna
Kasar Rasha ta kai wasu gagaruman hare-haren jiragen saman yaki marasa matuka ciki kan birnin Kharkiv na kasar Ukraine
Rasha ta kai wadannan gagaruman hare-haren ne ta hanyar amfani da jiragen saman marasa matuka ciki kan birnin Kharkiv na gabashin Ukraine. Magajin garin Kharkiv ya ce: Hare-haren da jiragen saman Rasha suka kai a tsakiyar birnin sun haddasa gobara da barna sosai.
Takaddama tsakanin Rasha da Ukraine na kara kamari a kasa duk da ci gaba da tattaunawa tsakanin bangarorin biyu ke yi. Mjiyar sojin Ukraine ta amince cewa: Sojojin Rasha sun kaddamar da gagaruman hare-hare kan birnin Kharkiv da ke gabashin kasar Ukraine ne, lamarin da ya haifar da fashe-fashe a birnin, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da jikkatan wasu, da kuma barnata kayayyaki, da kona gine-gine da dama, a cewar magajin garin Kharkiv.
Rundunar sojin saman Ukraine ta ce: Rasha ta harba jiragen sama marasa matuka ciki da suka kai 200, da makamai masu linzami guda biyu, da kuma wasu nau’ukan makamai masu linzami guda shida cikin kasar.
Kafin wannan harin dai an kai harin ne da wani kazamin makami mai linzami da na Rasha da aka kai a kan birnin Kiev babban birnin kasar Ukraine, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da jikkatan wasu.
Yayin da harin ya kawo cikas ga tsarin metro, a cewar mahukuntan kasar, shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelensky ya sanar da cewa: An kashe mutane da dama tare da jikkata wasu da masu yawa a cikin jami’an tawagar bayar da agajin gaggawa a hare-haren da suka hada da makamai mai linzami da jirage masu saukar ungulu a babban birnin kasar da kuma arewa maso yammacin birnin Lutsk, inda ya yi kira da a matsa lamba kan Rasha.