Aminiya:
2025-09-18@00:58:31 GMT

Matawalle ya yi wa Gwamna Lawal da wasu tayin shiga APC

Published: 8th, June 2025 GMT

Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya buƙaci Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, da ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Matawalle ya yi wannan kira ne a ranar Asabar, a garinsu Maradun, yayin da dubban magoya bayansa suka kai ziyarar gaisuwar Sallah.

Sallah: Gwamnatin Sakkwato ta bai wa kowane Alhaji kyautar N450,000 Gwamnatin Tarayya na shirin farfaɗo da kamfanin ƙarafa na Ajaokuta

Matawalle, wanda shi ne tsohon gwamnan Jihar Zamfara, ya ce APC jam’iyya ce ta mutanen kirki da masu kishin ƙasa.

Ya ce maimakon a ci gaba da takun-saka tsakanin gwamnati da ’yan adawa, zai fi kyau Gwamna Dauda ya fito fili ya rungumi jam’iyyar da ke da madafun iko domin ci gaban jihar da ƙasar gaba ɗaya.

“Idan Gwamna Dauda na da niyyar kawo ci gaba musamman a fannin tsaro da zaman lafiya, babu laifi ya zo ya haɗu da sauran ’yan kwamitin ci gaba a APC,” in ji Matawalle.

Matawalle, ya jaddada cewa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu na ƙoƙari wajen samar da zaman lafiya da ci gaban ƙasa, kuma yana buƙatar goyon bayan gwamnonin jihohi da sauran shugabanni don cimma nasara.

A baya-bayan nan, wasu ’yan siyasa daga jam’iyyun adawa da dama sun sauya sheƙa zuwa APC.

Sun bayyana cewa suna son su haɗa kai da Gwamnatin Tarayya wajen samun mafita ga matsalolin da ƙasar ke fuskanta.

Wannan na ƙara wa APC ƙarfi a jihohi da dama, ciki har da Zamfara.

Kiran da Matawalle ya yi wa Gwamna Dauda Lawal da wasu shugabannin adawa na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyyar APC ke ƙara karɓar sabbin mambobi daga jam’iyyun adawa, a wani yunƙuri na ƙarfafa tsarin mulki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamna Lawal matawalle Sauya Sheƙa Tsaro Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya

A daidaikun kasuwannin Abuja da wasu manyan birane na ƙasar nan, an bayyana yadda farashin doya ke ƙara hawa fiye da yadda ake tsammani.

 

Wannan na faruwa ne duk da cewa yanzu sabuwar doya ta fara shigowa kasuwa, bisa al’ada, a duk shekara fitowar sabuwar doya kan karya farashin wanda yake kasuwa. Sai dai a bana, wasu daililai na sa farashin doya kara hawa.

NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

wannan shine batun da shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba akai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago