HausaTv:
2025-07-23@22:38:02 GMT

 Rasha Ta Kai Wa Ukiraniya Hari Mafi Muni Tun Farkon Yaki

Published: 7th, June 2025 GMT

Sojojin Rasha sun kai hare-hare mafi muni akan cibiyoyin soja da muhimman cibiyoyi a kasar Ukiraniya da su ka hada da birnin Kiev.

Sojojin na Rasha sun yi amfani da kamamai masu linzami da jiragen sama marasa matuki masu kai harin kunar bakin wake da su ka haddasa tashin gobara.

Jami’in tafiyar da sha’anin Mulki a birnin Kharikiev ya bayyana cewa; A kalla mutane 10 su ka jikkata a bisa kididdigar farko.

 Ita kuwa rundunar sojan saman kasar ta Ukiraniya ta sanar da cewa; an yi amfani da makamai masu linzami samfurin “Cruise” wajen kai harin.

Su ma sojojin na Rasha sun sanar da cewa, sun kai wa Ukiraniya hare-hare akan sansanonin soja da kuma muhimman cibiyoyin kasar ta hanyar amfani da makamai masu linzami samfurin “Caliver” da kuma jirage marasa matuki.

A nata gefen ma’aikatar tsaron kasar Rasha ta sanar da kakkabo jiragen sama marasa matuki 82 da Ukiraniya ta harba daga cikin har da saman birnin Moscow.

Tun a makon da ya shude ne dai shugaban kasar Rasha, Vladmir Putin ya yi alkawalin mayar wa da Ukiraniya martani saboda hare-haren da ta kai wa wasu filayen saukar jiragen sama na soja da su ka hada wadanda suek dauke da muhimmanci jiragen yakin da Rashan take takama da su.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

WFP zai dakatar da tallafin abinci da kiwon lafiya a Nijeriya

Shirin Abinci na Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) ya bayyana cewa daga ƙarshen watan Yuli, zai dakatar da tallafin gaggawa na abinci da kiwon lafiya ga mutum miliyan 1.3 a Arewa maso Gabashin Nijeriya saboda ƙarancin kuɗi.

Darektan WFP a Nijeriya, David Stevenson, ya ce kayan abinci da na kiwon lafiya sun ƙare gaba ɗaya, kuma rabon da ake yi yanzu shi ne na ƙarshe.

Matasa 3 sun rasu yayin wanka a rafi a Bauchi 2027: Obi zai iya takara ba tare da ni ba — Datti Baba-Ahmed

Ya ce tallafin zai tsaya ne daga ƙarshen watan Yuli, lokacin da aka ƙiyasta kayan abinci da na kiwon lafiyar za su ƙare gaba ɗaya.

Idan ba a samu tallafi cikin gaggawa ba, mutane da dama za su fuskanci yunwa, gudun hijira ko kuma shiga hannun ‘yan tayar da ƙayar baya.

A cewar Mista Stevenson, kusan mutum miliyan 31 ke fama da matsananciyar yunwa a ƙasar wanda shi ne mafi muni a tarihi.

“Yara ƙanana za su fi shan wahala, domin fiye da asibitoci 150 a Borno da Yobe da ke kula da yara ’yan ƙasa da shekaru biyu za su rufe,” in ji daraktan.

WFP na buƙatar dala miliyan 130 domin cigaba da ayyukanta har zuwa ƙarshen shekarar 2025.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da tashe-tashen hankula ke ƙaruwa, kuma yunwa na kai matsayi mafi muni a tarihin ƙasar

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • WFP zai dakatar da tallafin abinci da kiwon lafiya a Nijeriya
  • Aikin Zirga-Zirgar Jiragen Sama Ta Fasinja Ta Sin Ya Bunkasa Zuwa Sabon Matsayi
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Na Isra’ila Da Makami Mai Linzami Nau’in Flasdinu
  • Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu
  • Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi
  • Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh
  • Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa
  • Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin
  • Jaridar Washington Post Ta Ce; Yeman Ta Gurguta Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Isra’ila
  • Ministocin Tsaron kasashen Rasha Da JMI Sun Hadu A Birnin Mosco