Jirgin ruwan na “Madeleine” shi ne na 36 a cikin jerin jiragen ruwan ‘yanci da suke son karya takunkumin da aka kakabawa yankin Gaza tun 2007.

A cikin wannan jirgin ruwan da akwai ‘yan gwgawarmaya masu rajin kare hakkin bil’adama su 12 da su ka fito daga kasashe daban-daban, yana kuma dauke da kayan agaji na abinci da magani.

 Jirgin ruwan ya samo sunansa ne daga wata Bafalasdiniya mai suna; Madeleine Kulaib, wacce ita ce macen farko ta Falasdinu da ta kware a sana’ar kama kifi bayan da mahaifinta ya yi shahada a yayin  yakin da HKI ta shelanta akan Gaza a 2023.

Jirgin ruwan na “Madline” ya taso ne daga kasar Italiya, wata daya bayan da jirgin sama maras matuki na HKI ya kai hari akan wani jirin ruwan wanda ya nufi Gaza akan gabar ruwan Malta.

Daga cikin kayan da jirgin ruwan yake dauke da shi a kawai madarar jarirai, shinkafa, da kuma magunguna da injinan tace ruwa. Haka nan kuma yana dauke da gabobin jikin dan’adam na roba na yara, saboda a yi wa yaran Gaza da Isra’ila ta mayar masakai dashe.

Mafi yawancin masu fafutukar dake cikin jirgin sun fito ne daga kasashen turai, kamar Sweeden Jamus da Faransa. Sai kuma wasu daga Holland da Brazil.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Jirgin ruwan jirgin ruwan

এছাড়াও পড়ুন:

Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro

“Muna bincike wannan lamari, kuma muna tabbatar da cewa duk jami’in da yake aikinsa bisa doka, za a kare shi. Ba za mu bari wani abu ya same shi (Yerima) ba matuƙar yana aikinsa yadda ya kamata kuma yana yin aikinsa sosai.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa November 12, 2025 Manyan Labarai Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna November 12, 2025 Manyan Labarai Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba November 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu
  • Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25
  • Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna
  • Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa
  • Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro
  • MDD ta sanya Najeriya cikin ƙasashe 16 da ke fama da tsananin yunwa
  • Ɗan Majalisar Wakilai daga Kano Sagir Ƙoƙi ya fice daga NNPP
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfado Da Filin Jirgin Sama Na Kano
  • Gaza : Isra’ila ta karya yarjejeniyar tsagaita wuta sau 282 tun bayan aiwatar da ita
  • Jakadun Kasashen Waje: Shirin Raya Kasa Na 15 Na Sin Na Dauke Da Kyakkyawan Sako