Jirgin Ruwa “Madeleine” Dake Son Karya Takunkumin Gaza Yana Ci Gaba Da Tafiya
Published: 8th, June 2025 GMT
Jirgin ruwan na “Madeleine” shi ne na 36 a cikin jerin jiragen ruwan ‘yanci da suke son karya takunkumin da aka kakabawa yankin Gaza tun 2007.
A cikin wannan jirgin ruwan da akwai ‘yan gwgawarmaya masu rajin kare hakkin bil’adama su 12 da su ka fito daga kasashe daban-daban, yana kuma dauke da kayan agaji na abinci da magani.
Jirgin ruwan ya samo sunansa ne daga wata Bafalasdiniya mai suna; Madeleine Kulaib, wacce ita ce macen farko ta Falasdinu da ta kware a sana’ar kama kifi bayan da mahaifinta ya yi shahada a yayin yakin da HKI ta shelanta akan Gaza a 2023.
Jirgin ruwan na “Madline” ya taso ne daga kasar Italiya, wata daya bayan da jirgin sama maras matuki na HKI ya kai hari akan wani jirin ruwan wanda ya nufi Gaza akan gabar ruwan Malta.
Daga cikin kayan da jirgin ruwan yake dauke da shi a kawai madarar jarirai, shinkafa, da kuma magunguna da injinan tace ruwa. Haka nan kuma yana dauke da gabobin jikin dan’adam na roba na yara, saboda a yi wa yaran Gaza da Isra’ila ta mayar masakai dashe.
Mafi yawancin masu fafutukar dake cikin jirgin sun fito ne daga kasashen turai, kamar Sweeden Jamus da Faransa. Sai kuma wasu daga Holland da Brazil.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Jirgin ruwan jirgin ruwan
এছাড়াও পড়ুন:
Sallah: Gwamna Inuwa ya yi kiran sadaukarwa da haɗin kai
Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya aika da sakon taya murnar Babbar Sallah ga al’ummar Musulmi, yana kira gare su da su rungumi darajoji na sadaukarwa, biyayya da hakuri irin wanda Annabi Ibrahim (AS) ya nuna.
A wata sanarwa da Daraktan Yada labarai na gidan gwamnati, Ismaila Uba Misilli ya fitar, Gwamnan ya yi kira da a yi addu’o’in zaman lafiya da haɗin kan Jihar Gombe da Najeriya baki ɗaya.
Ya jaddada muhimmancin nuna soyayya, tausayi da zama mai ƙyau da maƙwabta a rayuwar yau da kullum.
“Yayin da muke murnar Babbar Sallah, mu yi tunani kan abin da take nufi biyayya, sadaukarwa da ƙwarin gwiwa,” in ji Gwamna Yahaya, yana mai ƙarfafawa al’umma da su ci gaba da tallafa wa shugabanci a matakai daban-daban.
Gwamnan ya yaba wa shugabannin gargajiya da na addini bisa goyon bayansu tare da tabbatar da kudirinsa na kammala ayyukan ci gaba da aiwatar da sabbin manufofi masu alfanu.
Haka kuma, ya taya Alhazai Musulmi murnar kammala aikin Hajji, yana yi musu addu’ar dawowa lafiya da samun albarkar wannan ibada.