Aminiya:
2025-06-12@09:50:38 GMT

Saudiyya za ta fara bayar da bizar Umara

Published: 11th, June 2025 GMT

Bayan kammala aikin Hajjin bana, Saudiyya za ta fara bayar da bizar umara daga gobe Laraba.

Kazalika mahukuntan ƙasar sun ce dakatarwar shiga birnin Makkah ba tare da takardar izini ba zai ƙare daga ranar Larabar 11 ga watan Yunin 2025.

Dalilin da Nijeriya ke fuskantar tsaiko wajen karɓar rancen $5bn daga Saudiyya Gwamnan Kebbi ya bai wa ’yan kasuwar katako tallafin ibtila’in gobara

Ma’aikatar Hajji da Umarah ta Saudiyya ta ce za ta fara karɓar sabbin baƙi masu shigar ƙasar da bizar Umarah daga gobe Laraba, 11 ga watan Yuni.

Sanarwar na zuwa bayan kammala aikin Hajjin bana wanda kimanin mutum miliyan 1.6 daga faɗin duniya suka halarta.

Saudiyya takan dakatar da bayar da bizar umara makonni gabanin aikin Hajji domin bai wa mahukunta damar jiɓintar shirye-shiryen ibadar da ake gudanarwa duk shekara.

Wannan dakatarwar tana bai wa mahukunta damar mayar da hankali kan kula da hidimar mahajjata musamman a fannin tsaro, lafiya da sauran buƙatu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Saudiyya Umara

এছাড়াও পড়ুন:

Mokwa: Zulum ya kai ziyarar jaje Neja, ya bayar da tallafin N300m

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya kai ziyara Jihar Neja domin jajanta wa mutanen Mokwa da iftila’in ambaliyar ruwa ya shafa.

Zulum ya kuma bayar da tallafin Naira miliyan 300 domin taimaka wa waɗanda iftila’in ya shafa.

Ana zargin uwa da kashe ’yarta kan Naira 100 a Zariya Majalisar Dokokin Kuros Riba ta dakatar da shugabar ƙaramar hukuma na wata 3

Zulum, ya ce Gwamnatin Borno ta kawo wannan taimako ne don tallafabwa gwamnatin Neja wajen rage raɗaɗin ambaliyar da ta kashe mutane da lalata dukiyoyi.

Ya kuma buƙaci sauran gwamnatocin jihohi da ƙananan hukumomi su haɗa kai don kare al’umma daga iftila’i da sauyin yanayi ke haddasawa.

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya nuna godiya bisa wannan ziyara da tallafi.

Ya ce ya yi matuƙar farin ciki da irin wannan kulawa da ƙauna da Gwamnatin Borno ta nuna wa al’ummarsa.

Bago, ya tabbatar da cewa za a yi amfani da tallafin cikin gaskiya da adalci, tare da ci gaba da faɗakar da jama’a su guji gina gidaje a kusa da bakin kogi.

Zulum, ya samu rakiyar Sanata Mohammed Tahir Monguno, wasu ‘yan Majalisar Wakilai, Injiniya Bukar Talba, Hon. Abduljadir Rahis da mataimakin kakakin Majalisar Dokokin Jihar Borno, Injiniya Abdullahi Askira.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mokwa: Zulum ya kai ziyarar jaje Neja, ya bayar da tallafin N300m
  • Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon
  • Nijeriya Ta Fuskanci Cikas Wajen Karɓo Rancen Dala Biliyan 5 Daga Saudiyya
  • Iran Ta Fara Fidda Takardun Sirri Tsakanin HKI Da Hukumar IAEA
  • A hanzarta kwangilar yashe Madatsar Ruwa ta Alau — Gwamnatin Borno
  • A hanzarta kwangilar yashe Madatsar Ruwa ta Alou — Gwamnatin Borno
  • Dalilin da Nijeriya ke fuskantar tsaiko wajen karɓar rancen $5bn daga Saudiyya
  • Gwamna Zulum Ya Bayar Da Tallafin Miliyan 300 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Mokwa
  • Wani Kamfanin Kera Kayankin Aikin Likita Ya Gabatar Da Sabon Na’urar Tiyata