Saudiyya za ta fara bayar da bizar Umara
Published: 11th, June 2025 GMT
Bayan kammala aikin Hajjin bana, Saudiyya za ta fara bayar da bizar umara daga gobe Laraba.
Kazalika mahukuntan ƙasar sun ce dakatarwar shiga birnin Makkah ba tare da takardar izini ba zai ƙare daga ranar Larabar 11 ga watan Yunin 2025.
Dalilin da Nijeriya ke fuskantar tsaiko wajen karɓar rancen $5bn daga Saudiyya Gwamnan Kebbi ya bai wa ’yan kasuwar katako tallafin ibtila’in gobaraMa’aikatar Hajji da Umarah ta Saudiyya ta ce za ta fara karɓar sabbin baƙi masu shigar ƙasar da bizar Umarah daga gobe Laraba, 11 ga watan Yuni.
Sanarwar na zuwa bayan kammala aikin Hajjin bana wanda kimanin mutum miliyan 1.6 daga faɗin duniya suka halarta.
Saudiyya takan dakatar da bayar da bizar umara makonni gabanin aikin Hajji domin bai wa mahukunta damar jiɓintar shirye-shiryen ibadar da ake gudanarwa duk shekara.
Wannan dakatarwar tana bai wa mahukunta damar mayar da hankali kan kula da hidimar mahajjata musamman a fannin tsaro, lafiya da sauran buƙatu.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50
Ya sanar da cewa, manufar aikin ta faro ne, biyo bayan wata ziyarar aiki da Asusun ya ka Jihar Katsina.
“Asusun na NADF, ya dauki kwararan matakai; musamman ta hanyar zuba kudade don yin amfani da Dam din na Sabke da ke Jihar Katsina, domin yin amfani da ruwan da ke cikin Dam, don yin noma na zamani“, in ji Mohammed.
“OCP na Afirka, na da kwararru wadanda tuni suka auna yanayin kadadar da a gudanar da aikin, musamman duba da cewa; za a iya yin amfani da ruwan Dam din na Sabke, wajen gudanar da aikin”, a cewarsa.
Ya kara da cewa, Bankin shi kuma zai samar da wadatattun kudaden da za a yi aikin, wanda kuma Asusun na NADF zai kasance mai sanya ido kan aikin.
Ya kuma bayyana gamsuwar cewa, aikin zai kasance na zamani.
Shi kuwa a nasa jawabin, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Radda ya sanar da cewa; gwamnatinsa za ta bai wa aikin goyon bayan da ya dace.
“A lokacin da aka gabatar min da batun wannan aiki, nan da nan na aminta da shi, duba da irin dimbin alfanun da ke tattare da aikin, musamman wajen kara bunkasa tattalin arzikin Jihar Katsina da kuma rayuwar ‘yan jihar baki-daya“, in Radda.
“Burinmu shi ne, muga ana yin noma har zuwa gazayowar wata daminar a jihar, musamman domin al’ummarmu su kasance cikin shiri wajen gudanar da ayyuka a koda-yaushe tare kuma da amfana daga kudaden da aka kashe wajen sake gyaran wannan Dam da aka yi watsi da shi a baya”, a cewar gwamnan.
Shi kuwa a nasa bangaren, wakilin OCP na Afirka; Alik Orebaoghene ya sanar da cewa; gonar za ta kasance wajen bayar da horon sanin makamar aikin noma, musamman a tsakanin kananan manoma da ke jihar.
A karkashin wannan hadaka, ana sa ran OCP na Afirka zai samar da ingantaccen takin zamanin da za a gudanar da wannan aiki.
Shi ma, Manajan Daraktan Hukumar SRRBDA; Abubakar Malam, a nasa jawabin, jinjina ya yi kan kokarin da aka yi na sake farfado da wannan aiki.
Ya sanar da cewa, bisa tsarin kudurin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu (Renewed Hope Agenda), muna alfahari da samar da hektar noma daidai har guda 50, domin aiwatar da wannan aiki; musamman domin kara samar da wadataccen abinci a wannan kasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp