Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
Published: 7th, June 2025 GMT
Shugaban ya ci gaba da cewa, idan har zamu rage nauyin aikin da ke a kan Tashar ta Lekki, wajen biyan kudade, ya kamata ima Tashar ta san da cewa, muna da bukatar kudade da dama, domin mu sawo kayayyaki da dama na gudanar da ayyuka a Tashar, musamman domin mu tabbatar da cewa, ma’aikatan mu, na ci gaba da gudnar da ayyuakansu, a Tashar, kamar yadda ake bukata.
Dantso ya kara da cewa, za a yi aiki da tsarin NSW na kasa, inda zai samar da kaso 95 a cikin dari na gudanar da ayyuka a Tashar, wanda ya jaddada cewa, hakan zai kara rubunya, kudaden shiga, ga Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar.
“Gudanar da hada-hadar kudade ta hanyar yin amfani da na’ura, zai kawar da biyan kadade ta hanyar yin amfani, da rasidan bayan kudade, a daukacin Tashohin Jiragen Ruwan kasar, “ A cewar Shugaban.
“Idan hakan ya wakana, muna da yakinin cewa, za mu kara samun kudaden samun kudaden shiga masu yawa, kuma ina tunanin, za mu duba yuwuar, rage kudin shigar na fiton Jiragen Ruwan, “ Inji Dantsoho.
Shugaban ya kuma yabawa mahukuntan na Tsahar ta Lekki, kan bayar da daukacin gudunmawar su, domin ganin an kara daga martabar Tashar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Yi Ganawar Sirri da Gwamnonin Jihohi Shidda
Daga Bello Wakili
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi ganawar sirri da gwamnonin jihohi shidda daga sassan ƙasar a ci gaba da tattaunawar da ake yi domin ƙarfafa batun tsaro a ƙasa.
Gwamnonin da suka halarci taron sun hada da Gwamna Monday Okpebholo na jihar Edo, Umar Namadi na Jigawa, Nasir Idris na Kebbi, Ahmed Ododo na Kogi, Lucky Aiyedatiwa na Ondo, da Ahmed Aliyu na jihar Sokoto.
Taron, wanda ya ɗauki kusan mintuna 40, ya mayar da hankali ne kan muhimman matsalolin tsaro da ke shafar jihohinsu, duk da cewa ba a bayyana cikakkun bayanai ba.
Wakilin Rediyon Najeriya da ke fadar shugaban kasa ya ruwaito cewa wannan zaman na daga cikin kokarin shugaban kasa na ƙara haɗin kai da jihohi wajen magance matsalolin tsaro.
Wannan cigaban ya biyo bayan nasarar da Gwamnatin Tarayya ta samu na kubutar da dalibai 100 da aka yi garkuwa da su a Jihar Neja, baya ga wanda aka yi a Jihar Kebbi.
Ci gaba da irin waɗannan tattaunawa na shugaban kasa na nuna jajircewar gwamnati wajen tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin ƙasar.