Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
Published: 7th, June 2025 GMT
Shugaban ya ci gaba da cewa, idan har zamu rage nauyin aikin da ke a kan Tashar ta Lekki, wajen biyan kudade, ya kamata ima Tashar ta san da cewa, muna da bukatar kudade da dama, domin mu sawo kayayyaki da dama na gudanar da ayyuka a Tashar, musamman domin mu tabbatar da cewa, ma’aikatan mu, na ci gaba da gudnar da ayyuakansu, a Tashar, kamar yadda ake bukata.
Dantso ya kara da cewa, za a yi aiki da tsarin NSW na kasa, inda zai samar da kaso 95 a cikin dari na gudanar da ayyuka a Tashar, wanda ya jaddada cewa, hakan zai kara rubunya, kudaden shiga, ga Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar.
“Gudanar da hada-hadar kudade ta hanyar yin amfani da na’ura, zai kawar da biyan kadade ta hanyar yin amfani, da rasidan bayan kudade, a daukacin Tashohin Jiragen Ruwan kasar, “ A cewar Shugaban.
“Idan hakan ya wakana, muna da yakinin cewa, za mu kara samun kudaden samun kudaden shiga masu yawa, kuma ina tunanin, za mu duba yuwuar, rage kudin shigar na fiton Jiragen Ruwan, “ Inji Dantsoho.
Shugaban ya kuma yabawa mahukuntan na Tsahar ta Lekki, kan bayar da daukacin gudunmawar su, domin ganin an kara daga martabar Tashar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Magudnar Ruwa Ta Yi Ajalin Rayuka Hudu A Zangon Kaya, Kano
Mazauna unguwar Zangon Kaya da ke karamar hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano sun shiga cikin makoki sakamakon nutsewar da wasu matasa hudu suka yi a hanyar ruwa da baraguzan gine-gine suka tushe.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Saminu Yusif, ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin.
A cewarsa, lamarin ya faru ne bayan wadanda lamarin ya rutsa da su suka shiga mashigar ruwa da suka taru sakamakon toshewar hanyar jirgin da ake yi.
Ya kara da cewa, kamar yadda shaidun gani da ido suka bayyana, da farko biyu daga cikin wadanda abin ya shafa sun shiga cikin ruwan da nufin yin iyo amma sun makale. A kokarin ceto su, mutum na uku ya shiga, shi ma ya makale. Abin baƙin ciki, mutum na huɗu, yana ƙoƙari ya ceci sauran, ya fuskanci irin wannan matsalar.
Saminu ya yi nuni da cewa, kafin isowar hukumar kashe gobara mazauna yankin sun yi nasarar ceto biyu daga cikin wadanda abin ya shafa. Yayinda “Sauran biyun, tawagar ceto ta fito da
Wadanda abin ya shafa sun hada da Nasirudden Tasi’u dan shekara 25 da Basir Sani mai shekaru 28 da Yakubu Muhd dan shekara 22 da Usman Ubale dan shekara 26.
Jami’in hulda da jama’a ya yi nuni da cewa, an samu dukkanin mutane hudun a sume kuma daga baya aka tabbatar da sun mutu.
“An mika gawar su ga SP Abdulkadir M. Albasu na sashin ‘yan sanda na Dawanau domin ci gaba da bincike”.
Saminu ya ce, Daraktan hukumar kashe gobara ta jiha Alhaji Sani Anas ya jajantawa iyalan mamatan.
Ya kuma gargadi jama’a da su guji shiga cikin ruwa ba tare da izini ba ko kuma masu hadari, musamman wadanda ayyukan gine-gine ya shafa.
“Muna kira ga ‘yan ƙasa da su guji yin iyo ko wasa a cikin kududdufi, musamman waɗanda aka toshe ko ba a tsara su don amfani da nishaɗi ba.
Al’umma na ci gaba da nuna alhininsu yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike kan al’amuran da suka dabaibaye wannan mummunan lamari.
Rel/Khadijah Aliyu