Rasha Ta Kai Wasu Munanan Hare-Hare Kan Kasar Ukraine Tare Da Janyo Mata Munanan Barna
Published: 7th, June 2025 GMT
Kasar Rasha ta kai wasu gagaruman hare-haren jiragen saman yaki marasa matuka ciki kan birnin Kharkiv na kasar Ukraine
Rasha ta kai wadannan gagaruman hare-haren ne ta hanyar amfani da jiragen saman marasa matuka ciki kan birnin Kharkiv na gabashin Ukraine. Magajin garin Kharkiv ya ce: Hare-haren da jiragen saman Rasha suka kai a tsakiyar birnin sun haddasa gobara da barna sosai.
Takaddama tsakanin Rasha da Ukraine na kara kamari a kasa duk da ci gaba da tattaunawa tsakanin bangarorin biyu ke yi. Mjiyar sojin Ukraine ta amince cewa: Sojojin Rasha sun kaddamar da gagaruman hare-hare kan birnin Kharkiv da ke gabashin kasar Ukraine ne, lamarin da ya haifar da fashe-fashe a birnin, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da jikkatan wasu, da kuma barnata kayayyaki, da kona gine-gine da dama, a cewar magajin garin Kharkiv.
Rundunar sojin saman Ukraine ta ce: Rasha ta harba jiragen sama marasa matuka ciki da suka kai 200, da makamai masu linzami guda biyu, da kuma wasu nau’ukan makamai masu linzami guda shida cikin kasar.
Kafin wannan harin dai an kai harin ne da wani kazamin makami mai linzami da na Rasha da aka kai a kan birnin Kiev babban birnin kasar Ukraine, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da jikkatan wasu.
Yayin da harin ya kawo cikas ga tsarin metro, a cewar mahukuntan kasar, shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelensky ya sanar da cewa: An kashe mutane da dama tare da jikkata wasu da masu yawa a cikin jami’an tawagar bayar da agajin gaggawa a hare-haren da suka hada da makamai mai linzami da jirage masu saukar ungulu a babban birnin kasar da kuma arewa maso yammacin birnin Lutsk, inda ya yi kira da a matsa lamba kan Rasha.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Ukraine
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano Ta Maida Gidan Marayu Zuwa Cibiyar Gyaran Mata Masu Shaye
Gwamnatin Jihar Kano ta kara zage damtse wajen farfado da mata masu shaye-shayen miyagun kwayoyi ta hanyar mayar da Cibiyar Gyaran Matan Gaya, wadda a da ya kasance gidan marayu, zuwa wurin gyaran tarbiya.
Kwamishiniyar harkokin mata, yara da masu bukata ta musamman, Hajiya Amina Abdullahi Sani, ta jagoranci wata babbar tawaga zuwa cibiyar da ke Gaya domin tantance bukatun gyare-gyare da kuma hada kai da ma’aikatu domin gudanar da aikin.
Tawagar ta hada da kwamishinan ayyuka Engr. Marwan Ahmad Badawi, tawagarsa ta fasaha, daraktoci, da mataimaka daga ma’aikatar harkokin mata.
A yayin ziyarar, kwamishinar ta bayyana wa takwararta na ma’aikatar ayyuka irin ayyukan da ake bukata domin inganta cibiyar, da suka hada da gyare-gyare da fadada gine-gine domin daukar da kuma gyaran tarbiyar mata masu shaye-shayen miyagun kwayoyi a cikin yanayi mai aminci da tallafi.
A nasa jawabin, kwamishinan ayyuka Eng. Marwan Badawi ya bayar da tabbacin cewa ma’aikatar ayyuka za ta hada kai da ma’aikatar harkokin mata domin bayar da tallafin fasaha da ababen more rayuwa.
“Za mu tabbatar da cewa wannan ginin ya cika ka’idojin da ake buƙata don tallafawa yadda ya kamata don farfado da matan mu da ke fama da shaye-shayen ƙwayoyi,”
Tawagar ta kuma kai ziyarar ban girma ga mai martaba Sarkin Gaya, inda suka sanar da shi shirin gwamnatin jihar na yin wannan hubbasa.
Sarkin ya bayyana goyon bayansa tare da yabawa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa yadda ya bayyana a matsayin jagoranci mai hangen nesa da tausayi.
Gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta ci gaba da jajircewa wajen baiwa masu karamin karfi tallafi tare da samar da yanayi mai kyau na farfadowa da sake dawo da mutanen da suke fama da shan miyagun kwayoyi musamman mata.
Rel/Khadijah Aliyu