Rasha Ta Kai Wasu Munanan Hare-Hare Kan Kasar Ukraine Tare Da Janyo Mata Munanan Barna
Published: 7th, June 2025 GMT
Kasar Rasha ta kai wasu gagaruman hare-haren jiragen saman yaki marasa matuka ciki kan birnin Kharkiv na kasar Ukraine
Rasha ta kai wadannan gagaruman hare-haren ne ta hanyar amfani da jiragen saman marasa matuka ciki kan birnin Kharkiv na gabashin Ukraine. Magajin garin Kharkiv ya ce: Hare-haren da jiragen saman Rasha suka kai a tsakiyar birnin sun haddasa gobara da barna sosai.
Takaddama tsakanin Rasha da Ukraine na kara kamari a kasa duk da ci gaba da tattaunawa tsakanin bangarorin biyu ke yi. Mjiyar sojin Ukraine ta amince cewa: Sojojin Rasha sun kaddamar da gagaruman hare-hare kan birnin Kharkiv da ke gabashin kasar Ukraine ne, lamarin da ya haifar da fashe-fashe a birnin, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da jikkatan wasu, da kuma barnata kayayyaki, da kona gine-gine da dama, a cewar magajin garin Kharkiv.
Rundunar sojin saman Ukraine ta ce: Rasha ta harba jiragen sama marasa matuka ciki da suka kai 200, da makamai masu linzami guda biyu, da kuma wasu nau’ukan makamai masu linzami guda shida cikin kasar.
Kafin wannan harin dai an kai harin ne da wani kazamin makami mai linzami da na Rasha da aka kai a kan birnin Kiev babban birnin kasar Ukraine, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da jikkatan wasu.
Yayin da harin ya kawo cikas ga tsarin metro, a cewar mahukuntan kasar, shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelensky ya sanar da cewa: An kashe mutane da dama tare da jikkata wasu da masu yawa a cikin jami’an tawagar bayar da agajin gaggawa a hare-haren da suka hada da makamai mai linzami da jirage masu saukar ungulu a babban birnin kasar da kuma arewa maso yammacin birnin Lutsk, inda ya yi kira da a matsa lamba kan Rasha.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Ukraine
এছাড়াও পড়ুন:
Trump Ya Yabawa Rwanda Da Kongo DMK Kan Sulhuntawa A Yakin Gabancin Kongo
Shugaban kasar Amurka Donal Trump wanda ya jagoranci taron rattaba hannu kan yarjeniyar sulhuntawa da kuma kawo karshen yakin gabacin Kongo tsakanin shugaban kasar Rwanda Paul Kagame da tokwaransa na kasar Kongo Felix Tsetsekedi a birnin Washington a jiya Alhamis.
Shafinyanar gizo na labarai ‘AfricaNews” ya bayyana cewa, shuwagabannin biyu sun rattaba hannun kan wannan yarjeniyar ne a gaban kafafen yada labarai da dama a duniya. Kuma a ganin masana shugaba Trump yana neman suna ne kawai da wannan yarjeniyar.
Saboda babu tabbas kan cewa zaman lafiya zai dawo yankin Kivu na gabacin kasar Kongo. Banda haka, sun bayyana cewa hatta a dai dai lokacinda ake bikin rattaba hannu a kan yarjeniyar akwai labaran da suke tabbatar da cewa ana musayar wuta tsakanin kungiyar M23 da sojojin gwamnatin Kongo.
Banda haka kungiyar yan tawaye na M23 bata dauki shugaban kasar Rwanda a matsayin wakilanta a bikin na washingtopn ba. Sai dai akwai wani shirin zaman lafiya da take tattaunwa da gwamnatin kongo a kasar Qatar, inda suka cimma wani abu na ci gaba a tsagaita budewa juna wuta, amma bai kai ga rattaba hannu na din din din a tsakaninsu ba.
A karshen taron Trump ya ce Amurka da kasashen 2 zasu cimma wata yarjeniya ta hakar ma’adinai masu muhimmanci a kasashen biyu.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu December 5, 2025 Shin Ziyarar Putin a Indiya alama ce da ke nuna cewa New Delhi na yin watsi da gargadin Trump? December 5, 2025 Iran Ta Mayar Da Martani Kan Sanarwar Bayan Taron Majalisar Kasashen Yankin Tekun Fasha December 5, 2025 Afirka ta Kudu Za Ta Dauki Hutu Daga Halartar Tarukan G20 A Karkashin Shugabancin Trump December 5, 2025 Microsoft Za Ta Fuskanci Hukunci Kan Taimaka Wa Laifukan Isra’ila A Kan Falasdinawa December 5, 2025 Amurka Tana Sake Yin Bitar Alakar Da Ke Tsakaninta Da Tanzania December 5, 2025 Fadlallah Na Hizbullah Ya Yi Kiran Hadin Kai A Tsakanin Musulmi Da Larabawa Domin Fuskantar Kalubale December 4, 2025 Jiragen Haramtacciyar Kasar Isra’ila Sun Kai Hare-hare A Kudancin Lebanon December 4, 2025 An Kira Yi Gwamnatin Canada Da Ta Kama Olmert Da Livini Na “Isra’ila December 4, 2025 An Kashe Shugaban ‘Yan Dabar Gaza “Abu Shabab” Da Isra’ila Ke Goyon Baya December 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci