Leadership News Hausa:
2025-07-26@20:15:13 GMT

Ƙungiyar G-5 Ta Ceto Nijeriya Daga Faɗa Wa Rikici — Wike

Published: 10th, June 2025 GMT

Ƙungiyar G-5 Ta Ceto Nijeriya Daga Faɗa Wa Rikici — Wike

“Mun bi tsarin mulki kuma mun ƙi rashin adalci. Da PDP ta yi haka, ba za ta fuskanci wannan matsala ba.”

Taron ya haɗa da tsoffin gwamnonin jihohi Samuel Ortom (Benue) da Okezie Ikpeazu (Abia), da sauran shugabannin jam’iyyar.

Wike ya soki shugabannin PDP saboda sanya son rai fiye da haɗin kan jam’iyyar.

Ya ce jam’iyyar sai ta koma tubalinta na asali don samun ci gaba.

“Wasu shugabanni suna karkatar da dokoki don amfanin kansu,” in ji Wike, yana ambaton yadda gwamnan Taraba ya tsaya takarar gwamna ba tare da ya yi murabus a matsayinsa na shugaban jam’iyyar ba.

“Dole ne a daina wannan.”

Tsohon Gwamna Ortom ya yarda da maganar Wike, ya amince cewa PDP ta yi manyan kurakurai.

“Muna buƙatar taimakon Allah don gyara jam’iyyar,” in ji shi.

Ƙungiyar G-5 wadda ta haɗa da Wike, Ortom, Ikpeazu, Ifeanyi Ugwuanyi (Enugu), da Seyi Makinde (Oyo), sun yi adawa da takarar Atiku Abubakar a zaɓen 2023, wanda suka ce hakan ya saɓa wa dokar tsarin karba-karba.

Adawar ta jefa jam’iyyar PDP cikin matsalolin wanda hakan ya kai ta ga faɗuwa zaɓen 2023.

Yanzu, Wike yana aiki a ƙarƙashin Shugaba Tinubu amma har yanzu yana iƙirarin shi memba ne na jam’iyyar PDP, wanda ke ƙara dagula wa jam’iyyar lissafi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja

Idan har aka samu nasarar karɓar wannan gasa, za ta buɗe sabon babi a harkar wasanni da kasuwanci a Nijeriya, tare da samar da damammaki ga matasa da masu sana’o’i, da kuma ƙara haskaka ƙasar a idon duniya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
  • Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
  • Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato
  • Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja
  • Hulk Hogan ya mutu yana da shekara 71
  • Farfesa Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa
  • Gwamantin Kasar Siriya Ta Rufe Hanyoyin Shiga BirninSiweida Na Kasar Saboda Ci Gaba Da Bullar Rikici
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka sace
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 11 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Sakkwato
  • Nentawe Yilwatda ne zai zama sabon shugaban APC na kasa