Leadership News Hausa:
2025-06-13@17:04:18 GMT

De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City

Published: 12th, June 2025 GMT

De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City

An sanar da tashin shi daga City kafin karshen kakar wasa ta bana, kuma De Bruyne ya yi bankwana da magoya baya a filin wasa na Etihad bayan wasansa na karshe a gida da suka buga da Bournemouth a watan Mayu, City ta yi kokarin cike gibin da De Bruyne ya bari, yayinda ta dauki yan wasan tsakiya Tijjani Reijnders daga AC Milan da Rayan Cherki daga Lyon.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

 Iran Ta Sami Nasara Akan Korea Ta Arewa Akarkashin Share Fagen Shiga Gasar Cin  Kofin Duniya Na Kwallon

Kungiyar kwallon kafa ta Iran ta sami nasarar akan abokiyar karawarta ta kasar Korea Ta Arewa da kwallaye uku masu kyau a wasan da aka yi a filin wasa na “Azadi” na Tehran.

Kasashen biyu dai suna a karkashin; bangare na uku  a Asiya saboda share fagen kai wa ga shiga gasar cin kofin kwallon duniya na 2026.

Dan wasa mai suna Muhammad Muhibbi ne ya ci kwallon farko, a mintuna 74 da fara wasan, sai kuma Mahdi Darimi a mintuna 77, sa Amir Husain Husain zadeh, a minti 3 da aka kara, bayan cikar mituna 90.

A bangaren kungiyar kwallon kafa ta Korea Ta Arewa kuwa, ta kammala wasannin nata da ‘yan wasa 10 bayan da aka kori  daya daga cikinsu saboda adaidai mintuna na 66 daga fara wasa.

Sauran kungiyoyin da suke cikin wannan bangare na uku, da kuma su ka yi wasa a wannan rana, sun hada Uzbakistan da ta ci Qatar 3-0 a birnin Tashqand. Ita kuwa Kyrkizistan ta yi daya da daya da Hadaddiyar Daular Larabawa.

Iran ce a gaba a cikin bangaren nasu na uku; da take da maki 23, sai kuma  Uzbakistan mai binta da maki 21, ita kuwa Hadaddiyar Daular Larabawa tana da maki 15, yayin da Qatar take da maki 13. Kasar Kyrkizitan tana da maki 8, sai kuma Korea Ta Arewa mai maki 3.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Aliko Dangote Ya Sauka Daga Shugabancin Kamfanin Sukarin Dangote
  • Ya Kamata Ana Kammala Shari’ar Zaɓe Kafin Rantsuwa
  • Basaraken Da Aka Sace A Kogi Ya Kuɓuta Bayan Shafe Kwanaki 27 A Hannun ‘Yan Bindiga 
  • Tinubu Ya Soke Yin Jawabi Ga ‘Yan Kasa Na Ranar Dimokuradiyya, Zai Yi Daga Zauren Majalisa
  • Ɗan Ƙasar Indiya Da Wasu 12 Sun Gurfana A Kotu Kan Satar Wa Dangote Dizal Na Naira Biliyan 4
  • Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon
  • Tsohon Ɗalibi Ya Kai Hari Makarantarsu A Austria, Ya Kashe Ɗalibai 9
  •  Iran Ta Sami Nasara Akan Korea Ta Arewa Akarkashin Share Fagen Shiga Gasar Cin  Kofin Duniya Na Kwallon
  • Saudiyya za ta fara bayar da bizar Umara