Majalisar Dokokin Kuros Riba ta dakatar da shugabar ƙaramar hukuma na wata 3
Published: 11th, June 2025 GMT
Majalisar Dokokin Jihar Kuros Riba, ta dakatar da shugabar Ƙaramar Hukumar Bekwara, Hon. Theresa Ushie, na tsawon wata uku, domin a gudanar da bincike kan wasu zarge-zarge da ake mata.
An ce kimanin wakilan ƙaramar hukumar 10 daga cikin 11 ne suka yi ƙarar shugabar, inda tara daga cikinsu suka rattaba hannu suna goyon bayan a dakatar da ita.
Ɗaya daga cikin wakilan ne kawai bai yarda ba.
Ana zargin Hon. Ushie da amfani da kuɗin Ƙaramar Hukumar ba tare da shawarar majalisar jihar ba, tare da yin wasu muhimman ayyuka ba tare da tuntuɓar ’yan majalisar ba.
Mai magana da yawun Gwamnan jihar, Nsa Gill, ya bayyana cewa an dakatar da shugabar ne domin a samu damar yin cikakken bincike cikin kwanciyar hankali.
Shugaban majalisar dokokin jihar, Rt. Hon. Elvert Ayambem, ya ce an ɗauki wannan mataki ne bisa sashe na 14(3) na dokokin ƙananan hukumomin jihar da aka kafa tun 2005.
A halin yanzu, majalisar ta amince da naɗa mataimakin shugaban ƙaramar hukumar, Hon. Egbung Odama, a matsayin shugaban riƙo har zuwa lokacin da binciken zai kammala cikin wata uku masu zuwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: dakatarwa Shugabar Ƙarama
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya janye dokar ta-ɓaci da ya ayyana ta tsawon watanni shida a Jihar Ribas.
Tinubu, ya ayyana dokar tun a ranar 18 ga watan Maris, 2025, saboda rikicin siyasa da ya haifar da tsaiko a harkokin mulki tsakanin ɓangaren Zartarwa da Majalisar Dokokin jihar.
NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025 Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyiA jawabin da ya gabatar a Fadar Shugaban Ƙasa a ranar Laraba, Tinubu ya ce matakin dokar ta-ɓacin ya cimma manufarsa, kuma ba za a tsawaita ba ƙarewar wa’adin da aka gindaya.
“Ina farin ciki yau game da bayanan da ke hannuna, an samu yanayin fahimta a tsakanin dukkanin masu ruwa da tsaki a Jihar Ribas domin dawo da mulkin dimokuraɗiyya cikin gaggawa,” in ji Shugaban Ƙasa.
Gwamnan Jihar, Siminalayi Fubara, da mataimakiyarsa Ngozi Nma Odu, tare da ‘yan majalisar dokokin jihar, za su koma kan kujerunsu daga ranar Alhamis, 18 ga watan Satumba, 2025.
Tun da farko, dokar ta-ɓacin ta dakatar da manyan jami’an gwamnati da masu madafun iko na jihar sakamakon rikici da aka daɗe ana yi a jihar.
“Da ban ayyana wannan dokar ta-ɓacin ba, da hakan ya zama babbar gazawa a wajena a matsayina na Shugaban Ƙasa.
“Amma yanzu da zaman lafiya da doka suka wanzu, al’ummar Jihar Ribas za su sake cin moriyar dimokuraɗiyya,” in ji Tinubu.
Ya kuma yi kira ga gwamnoni da majalisun dokokin jihohi na faɗin Najeriya da su ci gaba da wanzar da zaman lafiya da haɗin kai tsakanin ɓangaren zartarwa da na majalisa.
Har ila yau, ya jaddada cewa zaman lafiya da kyakkyawan shugabanci su ne tubalin kawo ci gaban dimokuraɗiyya ga al’umma.