Majalisar Dokokin Kuros Riba ta dakatar da shugabar ƙaramar hukuma na wata 3
Published: 11th, June 2025 GMT
Majalisar Dokokin Jihar Kuros Riba, ta dakatar da shugabar Ƙaramar Hukumar Bekwara, Hon. Theresa Ushie, na tsawon wata uku, domin a gudanar da bincike kan wasu zarge-zarge da ake mata.
An ce kimanin wakilan ƙaramar hukumar 10 daga cikin 11 ne suka yi ƙarar shugabar, inda tara daga cikinsu suka rattaba hannu suna goyon bayan a dakatar da ita.
Ɗaya daga cikin wakilan ne kawai bai yarda ba.
Ana zargin Hon. Ushie da amfani da kuɗin Ƙaramar Hukumar ba tare da shawarar majalisar jihar ba, tare da yin wasu muhimman ayyuka ba tare da tuntuɓar ’yan majalisar ba.
Mai magana da yawun Gwamnan jihar, Nsa Gill, ya bayyana cewa an dakatar da shugabar ne domin a samu damar yin cikakken bincike cikin kwanciyar hankali.
Shugaban majalisar dokokin jihar, Rt. Hon. Elvert Ayambem, ya ce an ɗauki wannan mataki ne bisa sashe na 14(3) na dokokin ƙananan hukumomin jihar da aka kafa tun 2005.
A halin yanzu, majalisar ta amince da naɗa mataimakin shugaban ƙaramar hukumar, Hon. Egbung Odama, a matsayin shugaban riƙo har zuwa lokacin da binciken zai kammala cikin wata uku masu zuwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: dakatarwa Shugabar Ƙarama
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe mutum 15 a sabbin hare-hare a Filato
Rayukan aƙalla mutum 15 sun salwanta a wasu sabbin hare-haren da aka kai wasu ƙauyuka biyu na ƙaramar hukumar Mangu a Jihar Filato.
Shugaban ƙaramar hukumar, Emmanuel Bala, ya shaida wa manema labarai cewa, a daren ranar Talata ce aka kashe mutum bakwai a kauyen Bwai sai kuma mutane takwas a kauyen Chinchim duk a ƙaramar hukumar ta Mangu.
Mokwa: Zulum ya kai ziyarar jaje Neja, ya bayar da tallafin N300m Ana zargin uwa da kashe ’yarta kan Naira 100 a ZariyaWannan lamari na daga cikin sabbin hare-hare da tashin hankali da ke ci gaba da faruwa a yankin a wannan makon tsakanin yan kabilar Mwaghavul da Fulani.
Hare-hare daban-daban guda uku da suka faru a yankin ƙaramar hukumar Mangu a ranar Litinin da Talata, sun biyo bayan jerin hare-hare da ramuwar gayya da ake kyautata zaton sun fara ne yayin da mutane ke aikin haƙar ma’adinai a yankin da ke da arzikin Tin, a cewar shugaban ƙaramar hukumar, Emmanuel Bala.
Kamfanin Dillancin Labarai na AFP ta ruwaito Emmanuel Bala yana cewa, “Makiyayan Fulani Musulmai masu yawo da dabbobi sun daɗe suna samun saɓani da manoma da suke zaune a Jihar Filato — waɗanda mafi yawansu Kiristoci ne — kan rikicin mallakar fili da albarkatun ƙasa.”.
Ya ƙara da cewa hare-haren da ake kai wa a yankin sau da yawa na da nasaba da bambancin ƙabila da addini, wanda ke haifar da hare-haren ramuwar gayya marasa kakkautawa.
“Watanni da suka wuce, wasu mazauna yankin na aikin haƙar ma’adinai, sai aka kai musu hari da adduna, kodayake babu wanda ya mutu a harin farko.
“Amma bayan jerin ramuwar gayya da martani, an kai hare-hare uku a ranar Litinin da Talata, wanda ya yi sanadin mutuwar akalla mutum 20,” in ji Bala.
Wani jami’in Red Cross ya tabbatar da adadin waɗanda suka mutu cikin sa’o’i 24 a harin Chinchin, yana mai cewa adadinsu na iya kai wa 21.