Aminiya:
2025-06-18@02:27:25 GMT

Sabon Rikici: An kashe dan shekara 13 da wasu 3 a Filato

Published: 7th, June 2025 GMT

Akalla mutane hudu ne, ciki har da wani matashi dan shekara 13, an ce an harbe su tare da fille kawunansu a ranar Alhamis a yankin Gangaran Kwata da ke karamar hukumar Mangu ta Jihar Filato.

Mazauna yankin sun ce lamarin wanda ya faru da misalin karfe biyu na tsakar daren ya haifar da tashin hankali a yankin na Mangu.

Sojoji sun dakile hare-haren ‘Yan Boko Haram biyu a Borno Gwamnan Akwa Ibom ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC

Abdullahi Maicibi, shugaban addini a yankin Kwata, ya tabbatarwa da wakilin Aminiya faruwar lamarin, inda ya ce an dauki gawarwakin wadanda aka kashe zuwa babban masallacin Mangu da ke garin Mangu domin yin sallar jana’iza.

Shagari Madaki, another resident, said apart from the murders, many houses were burned during the incident, explaining that “We don’t know why the attackers invaded our area,” he added.

Wani mazaunin garin Shagari Madaki ya ce baya ga kashe-kashen da aka yi, an kona gidaje da dama a lokacin da lamarin ya faru, yana mai bayanin cewa “ba mu san dalilin da ya sa maharan suka mamaye yankinmu ba.”

A cewar shugaban addinin, wasu mutane dauke da makamai da ake zargin ‘yan kungiyar Mwaghavul ne suka mamaye yankin, inda suka yi ta harbe-harbe inda kashe mutum hudu.

Malamin addinin ya jaddada bukatar jami’an tsaro su dauki kwakkwaran mataki domin kamo wadanda suka aikata wannan aika-aika, yana mai cewa barin wadanda ba gwamnati ba su dauki makami a kan daidaikun mutane zai haifar da rashin bin doka.

Musa Ibrahim, kawun daya daga cikin mamatan, ya bayyana cewa suna tare da dan uwansa ne a lokacin da suka ji karar harbe-harbe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina

Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito cewa gwamnatin Jihar Katsina na ƙoƙarin sasantawa da wasu ƙungiyoyin ‘yan bindiga a wasu yankunan jihar.

Wasu daga cikin ‘yan bindigar da ke Jibia, Batsari da DanMusa sun amince da zaman lafiya tare da miƙa makamansu.

Sai dai wannan hari na baya-bayan nan ya sa al’umma sun fara shakkar ko zaman lafiyar zai ɗore.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka na iya kashe jagoran addini na Iran don mun san inda yake — Trump
  • Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina
  • Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga
  • Dan shekara 10 ya harbe mahaifinsa ɗan sanda a Anambra
  • Dan shekara 10 ya kashe mahaifinsa ɗan sanda da bindiga
  • Dakarun IRGC Sun Kakkabo Jirahen Yakin HKI Wadanda Ake Sarrafasu Daga Nesa A Lardin Zanjan
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe