Aminiya:
2025-09-17@22:14:43 GMT

Sabon Rikici: An kashe dan shekara 13 da wasu 3 a Filato

Published: 7th, June 2025 GMT

Akalla mutane hudu ne, ciki har da wani matashi dan shekara 13, an ce an harbe su tare da fille kawunansu a ranar Alhamis a yankin Gangaran Kwata da ke karamar hukumar Mangu ta Jihar Filato.

Mazauna yankin sun ce lamarin wanda ya faru da misalin karfe biyu na tsakar daren ya haifar da tashin hankali a yankin na Mangu.

Sojoji sun dakile hare-haren ‘Yan Boko Haram biyu a Borno Gwamnan Akwa Ibom ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC

Abdullahi Maicibi, shugaban addini a yankin Kwata, ya tabbatarwa da wakilin Aminiya faruwar lamarin, inda ya ce an dauki gawarwakin wadanda aka kashe zuwa babban masallacin Mangu da ke garin Mangu domin yin sallar jana’iza.

Shagari Madaki, another resident, said apart from the murders, many houses were burned during the incident, explaining that “We don’t know why the attackers invaded our area,” he added.

Wani mazaunin garin Shagari Madaki ya ce baya ga kashe-kashen da aka yi, an kona gidaje da dama a lokacin da lamarin ya faru, yana mai bayanin cewa “ba mu san dalilin da ya sa maharan suka mamaye yankinmu ba.”

A cewar shugaban addinin, wasu mutane dauke da makamai da ake zargin ‘yan kungiyar Mwaghavul ne suka mamaye yankin, inda suka yi ta harbe-harbe inda kashe mutum hudu.

Malamin addinin ya jaddada bukatar jami’an tsaro su dauki kwakkwaran mataki domin kamo wadanda suka aikata wannan aika-aika, yana mai cewa barin wadanda ba gwamnati ba su dauki makami a kan daidaikun mutane zai haifar da rashin bin doka.

Musa Ibrahim, kawun daya daga cikin mamatan, ya bayyana cewa suna tare da dan uwansa ne a lokacin da suka ji karar harbe-harbe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

 

A yayin samamen, kakakin ‘yansandan Neja ya ce an kama mutane shida a wurin da ake hakar ma’adinan yayin da wasu kuma suka tsere.

 

Abiodun ya bayyana sunayen wadanda ake cafken da Aliyu Rabiu, Samaila Ibrahim, Sadiku Auwal, Ibrahim Babangida, Musa Adamu da Sani Hassan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000