Aminiya:
2025-06-07@10:46:57 GMT

Sabon Rikici: An kashe dan shekara 13 da wasu 3 a Filato

Published: 7th, June 2025 GMT

Akalla mutane hudu ne, ciki har da wani matashi dan shekara 13, an ce an harbe su tare da fille kawunansu a ranar Alhamis a yankin Gangaran Kwata da ke karamar hukumar Mangu ta Jihar Filato.

Mazauna yankin sun ce lamarin wanda ya faru da misalin karfe biyu na tsakar daren ya haifar da tashin hankali a yankin na Mangu.

Sojoji sun dakile hare-haren ‘Yan Boko Haram biyu a Borno Gwamnan Akwa Ibom ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC

Abdullahi Maicibi, shugaban addini a yankin Kwata, ya tabbatarwa da wakilin Aminiya faruwar lamarin, inda ya ce an dauki gawarwakin wadanda aka kashe zuwa babban masallacin Mangu da ke garin Mangu domin yin sallar jana’iza.

Shagari Madaki, another resident, said apart from the murders, many houses were burned during the incident, explaining that “We don’t know why the attackers invaded our area,” he added.

Wani mazaunin garin Shagari Madaki ya ce baya ga kashe-kashen da aka yi, an kona gidaje da dama a lokacin da lamarin ya faru, yana mai bayanin cewa “ba mu san dalilin da ya sa maharan suka mamaye yankinmu ba.”

A cewar shugaban addinin, wasu mutane dauke da makamai da ake zargin ‘yan kungiyar Mwaghavul ne suka mamaye yankin, inda suka yi ta harbe-harbe inda kashe mutum hudu.

Malamin addinin ya jaddada bukatar jami’an tsaro su dauki kwakkwaran mataki domin kamo wadanda suka aikata wannan aika-aika, yana mai cewa barin wadanda ba gwamnati ba su dauki makami a kan daidaikun mutane zai haifar da rashin bin doka.

Musa Ibrahim, kawun daya daga cikin mamatan, ya bayyana cewa suna tare da dan uwansa ne a lokacin da suka ji karar harbe-harbe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

A wani cigaba makamancin haka, dakarun Mallam Fatori suma sun daƙile wani yunƙurin hari daga ‘yan ta’adda da suka zo ta wurare daban-daban.

Ya ce bayan sa’o’i na musayar wuta, dakarun sun bi ‘yan ta’addan da suka tsere, inda suka hallaka da dama, wasu kuma suka gudu da raunukan harbin bindiga. An kuma kwato muggan makamai da dama kamar bindigogi AK-47, da bindigar kakkaɓo jirgi (RPG), da sauran kayayyakin yaƙi. Yanzu haka Sojojin na ci gaba da sintiri a yankin, tare da goyon bayan jiragen sama da na leƙen asiri.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kashe Sojojin HKI Da Dama Sannan Wasu Sun Ji Raune A Garin Khan Yunus A Jiya Jumma
  • Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane
  • Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya
  • Mun gurfanar da mutum 29 a kotu kan zargin kashe DPO a Kano – ’Yan sanda
  • Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno
  • HOTUNA: Yadda ambaliya ta raba mutane da muhallansu a Mokwa
  • Direbobi sun toshe babbar hanyar Kogi sakamakon harbe abokan aikinsu
  • Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kashe Falasdinawa Wadanda Suke Jin Yunwa A Gaza
  • Jami’an DSS sun kashe ’yan bindiga 45 a Neja