Amurka Ta Sake Dorawa Iran Karin Takunkuman Tattalin Arziki Duk Tare Da Tattaunawa A Tsakaninsu
Published: 7th, June 2025 GMT
Gwamnatin kasar Amurka ta kara yawan takunkuman tattalin arzikin da take dorawa JMI dangane da shirinta na makamashin Nukliya.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa a wannan karon takunkuman sun shafi mutane 10 da kuma kamfanoni 27. Wadansu daga cikin kamfanonin suna kasar hadaddiyar daular Larabawa wasu kuma a Hong kong.
Ofichin Baitul malin Amurka ya bayyana cewa Kamfanin Ace Petrochem FZE da kuma Moderate General Trading LLC duk suna da rijister a UAE kuma kwace dukkan kadarorinsu da suke Amurka saboda wadannan takunkuman.
Labarin ya kara da cewa wadannan kamfanoni suna da dangantaka da kamfanin OFAC na kasar Iran, kamfanin tankunan jigilar man fetur.
Iran da Amurka dai sun gudanar da zagaye na 5 na tattaunawa a tsakanin kasashen biyu. Tun bayan ficewa Amurka daga yarjeniyar JCPOA a shekara ta 2018 ne Amurka take dorawa Iran takunkuman tattalin arziki.
A halin yanzu dai sabani ya shiga tsakanin kasashen biyu bayan da Amurka ta bukaci Iran ta kawo karshen tache Uranium a cikin gida wanda Iran tace ba zai yu ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Araghchi : Babu wata tattaunawa idan ba zamu tace uranium ba
Babban jami’in diflomasiyyar Iran ya sake tabbatar da cewa Iran ba za ta taba yin kasa a gwiwa ba kan ‘yancinta na tace Uranium, yana mai cewa ci gaban da kasar ta samu a fannin makamashin nukiliya ya samo asali ne sakamakon sadaukarwa da kuma saka hannun jari na kasa.
A cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi ya ce, ba batun inganta makamashin Uranium a duk wata yarjejeniyar nukiliya da za a yi nan gaba.
“Iran ta saka kudi da yawa domin kai wag a wannan mataki, sannan kuma ba zai sa mu yi watsi da sadaukarwar da ‘yan kishin kasa sukayi don tabbatar da burinmu.
Araghchi ya bayyana tace uranium a matsayin wani sakamako na ilimi da fasaha, mahimman abubuwan da suka ba Tehran damar habaka fasahar nukiliya cikin lumana duk da takunkumin shekaru da matsin lamba na kasa da kasa.
Yayin da yake bayyana matsayin Iran a tattaunawar da Amurka, ya kara da cewa: “Babu wata yarjejeniya idan ba zamu tace uranium ba, amma zamu iya cimma yarjejeniya wacce ta tanadi hana mallakar makamin nukiliya.”
Ya zuwa yanzu dai Iran da Amurka sun gudanar da jerin tattaunawa har sau biyar da nufin maye gurbin yarjejeniyar nukiliyar da aka cimma a shekarar 2015.