Gwamnatin kasar Amurka ta kara yawan takunkuman tattalin arzikin da take dorawa JMI dangane da shirinta na makamashin Nukliya.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa a wannan karon takunkuman sun shafi mutane 10 da kuma kamfanoni 27. Wadansu daga cikin kamfanonin suna  kasar hadaddiyar daular Larabawa wasu kuma a Hong kong.

Ofichin Baitul malin Amurka ya bayyana cewa Kamfanin Ace Petrochem FZE da kuma Moderate General Trading LLC duk suna da rijister a UAE kuma kwace dukkan kadarorinsu da suke Amurka saboda wadannan takunkuman.

Labarin ya kara da cewa wadannan kamfanoni suna da dangantaka da kamfanin OFAC na kasar Iran, kamfanin tankunan jigilar man fetur.

Iran da Amurka dai sun gudanar da zagaye na 5 na tattaunawa a tsakanin kasashen biyu. Tun bayan ficewa Amurka daga yarjeniyar JCPOA a shekara ta 2018 ne Amurka take dorawa Iran takunkuman tattalin arziki.

A halin yanzu dai sabani ya shiga tsakanin kasashen biyu bayan da Amurka ta bukaci Iran ta kawo karshen tache Uranium a cikin gida wanda Iran tace ba zai yu ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin

A yau Laraba kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya bayyana cewa aikin gina tashar samar da wutar lantarki ta karfin ruwa, a karshen kogin Yarlung Zangbo, aiki ne dake bisa ikon mallakar kasar Sin, kuma Sin din tana raya aikin don gaggauta samar da makamashi mai tsabta, da kyautata zaman rayuwar jama’ar wurin, da kuma tinkarar sauyin yanayi.

Guo ya ce, kasar Sin ta mai da hankali, da sauke nauyin dake wuyanta na amfani da albarkatun kogin da ya ratsa bangarenta da ma kasashen waje, kana tana da fasahohin gina tashar samar da wutar lantarki ta karfin ruwa. An tsara aikin ne a kan karshen kogin Yarlung Zangbo bisa ma’aunin Sin mai nasaba da aiki, da gudanar da aikin tare da kiyaye muhalli, da magance aikin a muhimman wuraren halittu don tabbatar da tsarin yanayin wanzuwar halittu. An gina tashar don magance bala’i a kan kogin, ta yadda aikin ba zai yi wata illa ga yankin karshen kogin ba.

Guo Jiakun ya yi nuni da cewa, kasar Sin ta yi hadin gwiwa tare da kasashen dake kan karshen kogin a fannonin sanar da yanayin kogin, da magance bala’i, da yaki da bala’i da sauransu, da kuma yin mu’amala da kasashen don ci gaba da yin hadin gwiwa da su, da kuma kawo moriya ga jama’arsu baki daya. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin
  •  Iraki Ta Yi Watsi Da Bukatar Amurka Akan Dakarun Sa Kai Na” Hashdus-sha’abi”
  • Pezeshkian: Tunanin Kawo Karshen Shirin Nukiliyar Iran Ya Yi Kama Da Tabuwa
  • Jami’an Kasashen Rasha, China, Iran Sun Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa A Tehran
  • Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa
  • Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar
  • Fizishkiyan: Batun Kare Hakkin Bil’adama Ba Komai Ba Ne Sai Karya
  • Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi
  • Jami’in Shari’ar Kasa Da Kasa Ya Bayyana Cewa: Harin Da Aka kai Kan Iran Babban Laifi Ne
  • Ministocin Tsaron kasashen Rasha Da JMI Sun Hadu A Birnin Mosco