Aminiya:
2025-07-04@23:59:15 GMT

Magidanci ya shiga hannu kan kashe matarsa mai juna biyu da duka

Published: 7th, June 2025 GMT

’Yan Sanda sun kama wani mutum mai suna Mohammed Sani mai shekara 31 da duniya, bisa zargin dukan matarsa Hauwa mai ɗauke da juna biyu, wanda ya zama ajalinta.

Lamarin ya faru ne a gidansu da ke unguwar Banin Hashim da ke Minna, a Jihar Neja.

Sojojin Isra’ila sun kashe mutum 13 a wajen rabon tallafi a Gaza 2027: Makomar Shettima a matsayin abokin takarar Tinubu na janyo cece-kuce

Hauwa mai shekara 24 a duniya wadda ke ɗauke da cikin wata tara, an same ta a mace a ɗakinsu kwance cikin jini.

Rundunar ’yan sandan ta samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 10:30 na daren ranar 3 ga watan Yuni, 2025.

Jami’an ‘yan sanda daga sashen A Division a Minna sun garzaya gidan.

Sun garzaya da Hauwa asibitin gwamnati da ke Minna, inda likitoci suka tabbatar da mutuwarta.

Haka kuma, likitoci sun tabbatar cewa tana da juna biyu.

Maƙwabtansu sun shaida wa ‘yan sanda cewa ma’auratan suna yawan samun saɓani, kuma suna zargin mijin ne ya yi wa matar dukan tsiya.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce an kama Mohammed Sani kuma an miƙa shi zuwa sashen binciken manyan laifuka na jihar (SCID) da ke Minna.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Rattaba Hannu Kan Daftarin Dakatar Da

Hadin Gwiwa Da Hukumar IAEA

Shugaban kasar Iran ya rattaba hannu kan dakatar da hadin gwiwa tsakanin Iran da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA, bisa wata doka da Majalisar Shawarar Musulunci ta kafa kwanan nan

Sanannen abu ne cewa: Wannan doka ta zo ne bayan hare-haren da Amurka da yahudawan sahayoniyya suka kaddamar da hare-haren wuce gona da iri kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran, a daidai lokacin da Iran ke shirin tunkarar tattaunawar nukiliya karo na shida da Amurka!

Har ila yau, an san cewa shawarar ba ta zama ficewa daga yarjejeniyar hana yaduwar makaman kare dangi ba, a’a, ta dakatar da duk wani nau’i na hadin gwiwa da hukumar kula da makamashin nukiliya ce ta IAEA har sai an cika wasu sharudda, musamman tabbatar da tsaron cibiyoyin makamashin nukiliya da masana kimiyya na Iran.

Harin da Amurka ta kai kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran, cin amanar diflomasiyya ce, da yarjejeniyoyin kasa da kasa, da dokoki. kuma wata mummunar yaudara ce da Trump ya cimma da hadi baki da Netanyahu don tauye hakkin Iran don kai harin. Da wannan ne Trump, wanda Netanyahu da jiga-jigan ‘yan sahayonyiya suka tunzura shi a Amurka, ya dauki matakin yin mummunar illa ga kima da martabar Amurka a duk duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Rattaba Hannu Kan Daftarin Dakatar Da
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Masu Neman Karbar Kayan Agaji A Gaza
  • SON Ta Bada Shaidar Ingancin Kayayyaki Ga Wasu Kamfanoni A Kaduna
  • Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Fitar Da Rahoton Wadanda Suke Taimakawa ‘Yan Sahayoniyya Wajen Murkushe Falasdinawa
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Fitar Da Rahoton Wadanda Suke Taimakawa Yahudawan Sahayoniyya Wajen Murkushe Falasdinawa
  • Lukurawa Sun Kashe Mutane 15 a Sakkwato
  • ‘Yan Sanda Sun Hana Yunqurin Fasa Shago a Gombe, Tare da Kwato Babur
  • Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar
  • Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang