Aminiya:
2025-11-03@07:57:24 GMT

Magidanci ya shiga hannu kan kashe matarsa mai juna biyu da duka

Published: 7th, June 2025 GMT

’Yan Sanda sun kama wani mutum mai suna Mohammed Sani mai shekara 31 da duniya, bisa zargin dukan matarsa Hauwa mai ɗauke da juna biyu, wanda ya zama ajalinta.

Lamarin ya faru ne a gidansu da ke unguwar Banin Hashim da ke Minna, a Jihar Neja.

Sojojin Isra’ila sun kashe mutum 13 a wajen rabon tallafi a Gaza 2027: Makomar Shettima a matsayin abokin takarar Tinubu na janyo cece-kuce

Hauwa mai shekara 24 a duniya wadda ke ɗauke da cikin wata tara, an same ta a mace a ɗakinsu kwance cikin jini.

Rundunar ’yan sandan ta samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 10:30 na daren ranar 3 ga watan Yuni, 2025.

Jami’an ‘yan sanda daga sashen A Division a Minna sun garzaya gidan.

Sun garzaya da Hauwa asibitin gwamnati da ke Minna, inda likitoci suka tabbatar da mutuwarta.

Haka kuma, likitoci sun tabbatar cewa tana da juna biyu.

Maƙwabtansu sun shaida wa ‘yan sanda cewa ma’auratan suna yawan samun saɓani, kuma suna zargin mijin ne ya yi wa matar dukan tsiya.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce an kama Mohammed Sani kuma an miƙa shi zuwa sashen binciken manyan laifuka na jihar (SCID) da ke Minna.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Wannan mataki ne awanni kaɗan bayan ɓangaren Damagum ya dakatar da Anyanwu da wasu mutane uku, lamarin da ya ƙara ta’azzaea rikicin shugabanci a cikin jam’iyyar PDP.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami November 1, 2025 Manyan Labarai Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su November 1, 2025 Manyan Labarai Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda matata ta ɓace a Abuja aka tsince ta a Sakkwato
  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  • Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare