Wani rahoto na gungun kwararru da aka fitar a Lahadin nan, ya nuna yadda kasar Sin ke ta kokarin samar da kyakkyawan yanayin zaman lafiya, da kawance, da hadin gwiwa a yankunan tekun kudancin kasar.

Rahoton na kwararrun cibiyar Xinhua, mai alaka da kamfanin dillancin labarai na kasar Sin wato Xinhua, na da lakabin “Mayar da tekun kudancin Sin wuri mai cike da zaman lafiya, kawance da hadin gwiwa: matakan da Sin ke dauka”, ya ce har kullum Sin na nacewa matakan wanzar da zaman lafiya, da daidaito a yankunan tekun kudancin kasar, kuma nasarar hakan na da alaka da matakan hadin gwiwa da ake aiwatarwa tsakanin Sin da kasashe mambobin kungiyar ASEAN.

Rahoton ya kara da cewa, ta hanyar zurfafa amincewa da juna, da hadin gwiwa mai game da dukkanin sassan siyasa, da tattalin arziki, da al’adu, wannan hadaka ta samar da wani yanayi na cimma moriya mai dorewa ta bai daya. Sakamakon hakan, Sin ta zamo karfi abun dogaro dake wanzar da zaman lafiya da daidaito a shiyyarta, yayin da take ta ingiza hadin gwiwa da ci gaban yankin tekun kudancin kasar.

Har ila yau, Sin ta yi aiki tukuru wajen gina zaman lafiyar shiyya, ta hanyar amincewa da juna ta fuskar siyasa, da bunkasa cin moriyar tattalin arziki na bai daya, domin tabbatar da walwala a shiyyarta, da inganta dinkewar al’ummu, ta yadda za a cimma makomar bai daya. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: tekun kudancin kasar da hadin gwiwa zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya

Kwamitin kasa mai lura da kasuwancin Amurka da Sin ko USCBC, ya gudanar da liyafar murna ta shekarar 2025, a ranar Laraba 18 ga wata a birnin Washington na Amurka, liyafar da jakadan kasar Sin a Amurka Xie Feng ya halarta tare da gabatar da jawabi.

Cikin jawabin nasa jakada Xie ya ce cimma moriya da nasara tare, muhimman ginshikai ne na ci gaba mai dorewa na hadin-gwiwar Sin da Amurka ta fuskar raya tattalin arziki da kasuwanci, inda dukkan bangarorin biyu gami da duniya ke cin gajiya. A halin yanzu, habakar tattalin arzikin duniya na tafiyar hawainiya, kuma kara hada kai ita ce mafita daya tilo ta shawo kan hakan. Ya ce ci gaban kasar Sin zarafi ne ga dukkanin duniya baki daya, wato yarda da kasar Sin tamkar yarda da kyakkyawar makoma ne, kuma zuba jari a kasar zai haifar da babbar nasara a nan gaba.

Jakadan ya kara da cewa, dangantakar Sin da Amurka na cikin wani muhimmin lokaci, kana, neman hada kai don cimma moriya tare, ko kuma nuna wa juna kiyayya, hanyoyi ne mabambanta dake gabansu. Don haka ya dace kasashen biyu su tsaya bisa jagorancin shugabanninsu kan manyan tsare-tsare, da aiwatar da muhimman ra’ayoyi iri daya da suka cimma a zahiri. Har kullum kasar Sin na nuna sahihanci amma mai kunshe da sharadi, wato kiyaye cikakken yankin kasa, gami da muradun neman ci gaba, tamkar jan layi ne da ba za a iya tsallakewa ba, yayin da girmama juna, da kiyaye zaman lafiya da samun moriya tare cikin hadin-gwiwa, suka zamo babbar ka’ida da dole a mutunta ta. (Murtala Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
  • Firaministan Singapore: Jama’ar Sin Suna Da Kwarewar Kirkire-Kirkiren Fasahohi
  • Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna
  • Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia
  • Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka
  • Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya
  • Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato
  • Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiya
  • An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming
  • Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho